Featured

Own A Blog Like This
For Questions, Inquiries, Click Here
Page | Group - Follow us - Call us - Hire Us - usamaumarusman1@gmail.com

DAGA DAKIN GIRKI

Girkinki shine kimarki
Tabbata kin kiyaye kimarki tahanyar kyautatawa iyalinki
    Kikasance uwa abar alfahari tahanyar gyara girkinki kalli daga wannan

DOWNLOAD
Read More »

Hausa nobles

Domin nishadi da walwalacikakken labarin littafi maisuna
ABINDA AKE GUDU
Domin karanta wanan qayataccen littafi danna wagga download
Read More »

Asian movie

Kung-Fu Yoga 2017
Genre: Action, Adventure, Comedy

Two professors team up to locate a lost treasure and embark on an adventure that takes them from a Tibetan ice cave to Dubai to a mountain temple in India.
Download
Read More »

Movies series

IRON FIST S01E04

Download
Read More »

Movies series

IRON FIST S01E03

Download
Read More »

Movies series

IRON FIST S01E02

Download
Read More »

Movies series

IRON FIST S01E01
After his family meets a tragic fate while on expedition in China, a young Rand is adopted by the people of the mystical lost city of K\’un-Lun, where he\’s taught a magical fighting style. Years later, he returns to New York to fight crime.
Download
Read More »

Korean movie

 Sanada Ten Braves 2016
Cast
nkurô Nakamura, Tôri Matsuzaka, Yuko Oshima
Download-bluray
Read More »

Movies series

INTO THE BADLANDS S02E02
Sunny and Bajie struggle to stay alive; the Widow consolidates her power in the face of challenges.
Download
Read More »

NA MANTA KOMAI Part 6

NA MANTA KOMAI Part 6
.
Bayan sun kusa gida, ya tsaya ya yi musu siyayyah, gurin
bata ledar hannayensu suka had'u dana juna, saida yaji
wani iri, sun iso gida, ta wuce d'akinta, biyo bayanta ya yi
ba tare da ta sani ba , tana k'ok'arin cire kayan jikinta, ya
shigo d'akin, duk da cewa taji wani iri daya ganta ba wasu
tufafin, sai kuma tace mi zan boyewa mutumin da ya dad'e
da sanina hadda yaran mu biyu...
.
Ahmad kam yaji wani iri, yad'an sosa kai ya duk'ar da
kanshi k'asa dan yaji wani iri sosai, gashi ya dad'e ba mace
tun bayan rasuwar matarsa, ya zauna sai ya juya mata
baya dan yana gudun kar a samu matsala. Saida ta k'are
saka kaya ta na neman hanyar fita, Yace "Suhailah baki
tambayi result din hospital d'inki ba?" Tace "to ai na san
zaka gaya mani indai na in sani ne", ta d'an yi murmushi,
da alama ta d'an saki jikinta, ya ce "kin d'an samu accident
ne ki ka buga kanki, shine kuma ya ja maki wannan lost of
memory din, amma Dr. ya tabbatar mani da cewa zaki
koma normal cikin d'an lokaci kad'an, dan haka karki tada
hankalinki kinji?", ya fad'a yana kallon ta, "kinga yanzu
saboda haka ne na ke so in kai ki Holland dan a k'ara
dubaki, in sha Allah nan da kwana biyu zamu tafi," wasu
kwalla suka zubo daga idanuwanta, tasa bayan hannunta ta
goge, ta dago kai ta dubeshi ta ce "to na gode", harda
murmushin karfin hali, har ya mik'e zai fita tace "dan Allah
ka gaya mani wani abu about My self kila zan tuna,"
hakikanin gaskiya, tun lokacin da hannayensu suka had'u
ya farajin sha'awar da ya dad'e baiji irinta ba, kusan tun
rasuwar matarshi baya da lokacin mace, aikinshi kawai
yasa gaba da binciken abubuwan dake faruwa da wa'danda
suka faru a baya, ga addini ya rik'e hannu biyu , mafari
kenan Alhaji Ibrahim yayi sha'awar hadashi da Suhaila dan
Ahmdy akwai addini . "Zan gaya miki amma saida safe". Ya
tashi ya wuce dakinshi, amma kuma ogan naku ya kasa
sukuni, gashi an dad'e ba'a haduba, ya fito da niyyar ya
d'an kalli fuskarta ne kawai, amma sai ya isketa ido biyu,
yasan matarshice halaliyarshi, amma sai da yaddarta, da
kuma lafiyarta ya ke son ya kusanceta, kuma yanzu gashi
har tunani take wai ta haifa mashi yara, zayyi k'ok'ari ya
danne sha'awarshi har yaga ta dawo cikin hankalinta kafin
ya kusanceta a matsayin matarshi, alk'awarin da yayi ma
kanshi kenan To ko zai iya kuwa?? Har wata zuciya ta bashi
shawarar ya koma d'akinshi abunshi, amma sai ya kasa
yazo yace "to matsa mani na kwanta", zuciya d'aya tunda
gani take komai ya riga ya faru ta yaye bargo ta matsa
mashi ya zauna kusa da ita, ya kasa kwanciya sai ya jingina
da gadon, yace "to daga ina zan fara" ya fada yana
Murmushi, a lokaci d'aya ya jawo bargo ya lullube k'afarshi,
ta matsa kusa dashi sosai tace "babana shine wanda yazo
ko? mamana da k'anena sune wayanda nayi waya dasu ko?
To Ina da yayye?" ya yi dariya sosai yace "kinason family
da yawa kenan?", ta zaro ido "bani dasu ne?
.
Ko ba sune nawa ba", yadda tayi ya bashi dariya, kallonshi
take sosai ta cire bargon ma sama daga jikinta ta
lank'washe k'afafuwanta, ita hankalinta kwance da yar rigar
baccinta, shara shara, ya d'auke idonshi da kyar daga
kallon duk inda jikinta ya bayyana, dan kayan baccinta
kamar yar singleti ce da short wando rabin cinya gasu
shara-shara. Ahmad ya samu kanshi da rik'o hannunta,
kamar zata anshe sai kuma ta bar shi ya rike tunda
mijintane, ya yi murmushi ganin ta amince da hakan, ya ce
kina da yaya d'aya Ameen, kina da abokin haihuwa Suhail,
ke kuma sunanki Suhailah, ku twins ne," "laaa shi isa na
haifi twins", ya dai bata dan labarin da ya sani game da ita
da asalin babanta da mamanta, yana kauce ma duk wani
abunda zai sosa mashi rai, dan labarin family dinta ba a iya
rabashi da na family din shi, tace "to na ji na wa, saura na
ka, a ina mu ka hadu da kai, har mukayi aure?" Ya ji wani
rass gabanshi ua fad'i, yace "kibari zaki tuna a hankali, "Pls
ka gaya mini," ta wani langwabe kai ta matsa jikinsa sosai,
tare da d'an matse hannunshi da nata cikin shagwaba tana
wani farfar da ido, mutumin fa ya fara daukar zafi, ya na
jan nunfashi da k'arfi yana fitarwa, ya runtse idanuwanshi
yana neman natsuwa, ya bud'e bayan d'an lokaci kad'an
yace "mun had'u tun da dad'ewa bayan nan mun k'ara
haduwa a bikin su Al- Ameen sai daga baya kuma mukayi
aure," tace "yauwax", ta k'ara matse mishi hannu, "to wayafi
son wani ni da kai?", bai amsa tambayar ba ,saboda ya
aureta ne dan mahaifinta ya ba shi ita, "yaranmu yan biyune
ko,? D'azu kace min maman twins haka kake kirana
dama?",yace kin cika tambaya, tace "da banida yawan
tambata hala?", Ya daga mata kai, dan ya riga ya d'au zafi
ko magana baya son yi, ta ce ''to na daina", ya ce "ya akayi
baki mance da sallah ba?", ya tambayeta dan ya ji tana ce
ma yaran su zo su yi sallah, tace "wallahi ban sani ba," to
Ina son ki natsu kiji abunda zan gaya maki, "Suhailaa you
are a Doctor," ai sai ta mik'e kan gado tana tsalle da rawa,
shiyasa taga wani k'aton littafi a cikin kayanta wai shi
"internal medicine," duk sadda ta samu lokaci tana
karantashi, data natsu ya kamo hannunta yana magana a
hankali kamar baya so, yace "bani son kowa yasan kin
samu wannan matsalar dan kar ya jawo maki matsala a
gaba, dan haka kar ki gaya wa kowa, kinji?", gobe zamu kira
su mama ki k'ara gaishesu kuma kiyi masu sallama, jibi
zamu tafi", tace "to In sha Allah ba wanda zai ji....
.
Suhaila yarinya ce mai ban sha'awa, bare kuma yanzu da ta
ke cike da farin ciki ganin mijinta ya dawo mata, kawai sai
ya ji ta rungumeshi ta ce na gode, shima ya rungume ta
yana shak'ar k'amshinta da ya bai baye ko ina cikin d'akin.
a hankali ya ke neman natsuwa, amma tana neman ta rikita
mashi lissafi, ya runtse idanuwanshi. Dai-dai kunnenshi ta
ce "wane suna nake kiranka dashi, Ahmad haka nake
kiranka ko?" Dak'er ya daure cikin natsuwa ya ce "sai ya ce
sunana kenan ai," ta ce "amma nima haka nake kiranka
dashi?" "No" ya fada ya na d'an murmushi. "To ya nake
kiran ka dashi?" Ta tambaya. "kar ki damu za ki tuna yanda
kike kirana". "Ok, yanzu tell me about you," tana k'ok'arin ta
tashi zaune daga d'an kwantawar da tayi a jikinsa, aranshi
yavce wannan yarinya akwai jaraba, ta k'ara gyara
zamanta tana kallonshi. "To....."
.
Ya katseta, ya ce aa, ya isa haka, ki kwanta kiyi bacci dare
yayi sosai,da kanshi ya gyara mata kwanciya, ya lullubeta,
ya mik'e zai tafi, har zai tafi ta rik'o hannunshi, "please ka
kwanta dani, ko dan banida lafiya kake guduna ko kuma
dama ba tare muke kwana ba!? "Innalillahi! Wannan
yarinyar so take ta kasheni" abunda ya fad'a kenan a
zuciyarshi, ta jawoshi tare da matsa mashi, inda zai kwanta
kusa da ita, "oya zo ka kwanta" haka ya samu kansa da
kwanciya inda ta matsa mashi. Tunani ya ke ya san fita da
ita zuwa k'asar Holland bazai masa wuya ba, dan yasan
can sosai, visa ma ba zaya sha wuyar samu ba tunda ya
zauna can ya dad'e, kuma ya na da mutane da yawa acan.
Bawan Allah Ahmad sai gaf da asuba bacci yayi awon gaba
dashi, dak'er ya tashi yayi sallah, Sannan ya tashi Suhailah,
itakam duk da tajita daban kamar ba ta saba da irin hakan
ba da suka kwanta ya rungumeta, amma tayi bacci mai
dad'i, ta bar shi akan dan ta manta komai ne yasa ta ke jin
hakan, suna had'a ido ta masa murmushi, itakam gani take
kamar ta fishi sonsa, amma so take ta danne har ya gaya
mata gaskiya wayafi son wani ita dashi. Tayi alwala tayi
sallah, ta nemi guri ta kwanta amma sai taga Ahmad zaune
yanata lazimi, tadan matso kusa dashi, tace "nima ina
wannan zaman bayan salla asuba ada!?" Yayi mata
murmushi, sai ta kanne masa ido, yayi sauri ya kawar da
ganinsa gareta, yace "wani lokaci kinayi wani lokaci kuma
bakya yi," tace "heheeeee irin yaune banayi dan kuwa bacci
zanyi, ta dubeshi, ka mini addu'a na haifi namiji, tunda
inada mata har biyu," baice mata komaiba, hasali ma kasa
lazimin yayi dan sai hada masa zafi takeyi, tazo gefensa ta
kwanta.!
.
***********
Rannar ya dawo gida da wuri, ba kamar da ba, da sai tayi
bacci, yanda Ahmad ke son yaransu ya birgeta sosai, taji ta
k'ara sonsa tunda yanason yaranta, yau kam duk tare
sukaci abinci rana da ita dashi da yaran su, yaran sam
sukak'i yadda su ci su kad'ai, wai sai sunci abinci tare da ita
a plate d'aya ganin Ahmad na murmushi yasa ta biye masu,
suka cinye har suka k'ara, bayan sun k'are 'yar bak'a ta
kwashe yaran da kwanuka, bayan sun gama tayi masu
shirin bacci, ita kuma Suhaila ta gyara inda sukaci abincin
har Ahmad d'in na tayata, sai abin ya burgeta, aranta tace,
"kilama ada haka mukeyi, Ashe dai mijina ya had'u, yauma
sau biyu hannunsu na haduwa, garin wanke kwanuka, inda
suhaila kejin wani irin sak'on da bata saba jiba na mata
yawo a kowace kafa ta jijiyoyin jikinta, batajin dad'in hakan,
sai taji kamar ta bar mashi aikin kawai. Wajen bacci ma
haka yaran suka nace su da Dady zasu kwana, ba wayonda
ba'a musuba amma sukak'i yarda. Haka Suhailah tayi ta
juyi ita adai a gado ta kasa bacci, dan ta saba tun randa
tazo tare suke kwana da yaranta sai jiya da sukaje asibiti
suka kwana da Ahmad, yanzu gashi ba yaran ba uban,
tsaki tayi ta juya har ta fara bacci. Can cikin dare taji an
bude kofar d'akinta an shigo har taji dadi a zatonta su
Surayya ne, murmushin dake fuskarta tuni ya bace ganin
Ahmad har ya karaso gaban gadonta, nan suka tsaya suna
kallon kallo, na dan wani lokaci sannan ya zauna daga
gefen gadon, tuni ta gyara zamanta ta matsa dayan gefen
gado, yace "miye haka kuma!? Da sauri ta k'irk'iro
murmushi tace "laaa ba komai, zo ka zauna ta na k'ok'arin
janyo hannunsa.......

Read More »

***** SAMRA 6 *****

***** SAMRA 6 *****
.
Bayan tagama hada kayan tashiga bayi ta kara watsa ruwa
....tana fitowa tayi light makeup tafeeto...tunda tafeeto
yake binta da ido kamar zai cinye ta....ta xauna a kasa
kusa da kafan shi tace abba nagama yace kk tashi
muje..tayi gaba tana tafeeya can yakirata tadawo baya
yace bby meyasa yanxun baki son zama kusa dani kamar
da tayi shuru yace kunya na kikeji bby ta daga kanta kawai
sama...yayi darya yajasu xuwa gdan suna shiga cikin gdan
yayi gaba ita kuma tana biye dashi suka shiga pallow .....ya
xauna akan kujera itakuma akasa ..
.
Yakalleta yayi murmushi kawai yace bby xa innuna miki
dakin ki nikuma inwuce masallaci tace toh ....Bayan
yadawo daga masallaci ya shigo dakinta ita kuma daidai
lkcn tafeeto daga bayi kenan bata san mutum yana gun ba
kawai sai taga mutum takulle idonta tana salati...shiko
dayaga ta dan tsorata sai ya tashi ya matso kusa da ita
tana bby abbankine fa dakyar tabude idonta....dayaga
tasami natsuwa yace inta gama tasameshi adakin
shi....daya gan she ix confused yace xo innuna miki
dakin....yadan bude kofan ya mata pointin sannan ya tafee
itakuma takoma taje tashirya.
.
Bayan tagama naje sata shiga dakin shi....amma sai
takasa can tayi sallama tashiga amma saita ga bakowa can
saitaji karan ruwa abayi allamun mutum na wanka
abayi...haka taxauna asamar gado ....bayan minti 10 da
xamanta agurin sai gashi nan yafito daga bayi da boxers
duk kunya yarufeta ....ya kalleta yayi murmushi aranshi
yace yarinya xakiyi bayani ne......haka yagama duk abunda
xayyi ma matso kusa da ita yace bby tunda na dawo bamu
samu damar mgna ba ....tadaga kai yace oyya tel me wat
appnd wen i was away frm home...tace abba kasan bana
xama a gda only wen am on holiday......
.
yace so tel wen u were on holiday wat appnd....tace abba
gasky anty nafee bata kyauta maka sbda alkcn idan tafeeta
da daddare ko da safe bata dawowa sai the followin day
nikan rasa inda take xuwa.....amma abunda tamin sai
ALLAH ya mata ...abba kasan duk hutun daxamuyi idan
nadawo gda bata bani abinci thrghr out har in tafi saidai
ingirka ko inje gdan matar tahir haka dai yayi ta lallashinta
...tare da mata nasihohi sannan yajawo ta yace su
kwanta...ya jawota kirjinshi alkcn duka jikinta yasoma
rawa...can kawai yasaka bakinshi cikin nata ...sun kai
olmost 30mint yana kissin dinta...
.
Can kawai yasoma gangarowa xuwa kasa.. daga nan kam
sai kirjinta tana jin haka takwaci bakinta murya narawa tace
abba kabari shiko bai ma bari tagama mgna ba kawai
yakara cafko bakin yana tsotsa kamar yagan sweet.....nan
fa yahau matse kirjinta yasona cire mata rigarta ...yayi
nasarar cire mata rigarta yabarta kamar yanda uwarta ta
haifeta sai daya gama mata kallo saf....shiko ajikin ta ba
abunda yafi burgeta kamar kirjinta ....nan fa yasa baki
yasoma suckin ......itako sai kuka takeyi.....can kawai
wayar shi yasoma ringin yadauka yace alhji ina yini yace
duk inda kuke gobe kuxo gda gobe ashe dai samra cousin
sister dinka ce...nan wayar yafadi ahannun sadeeq sbda
abunda yaji...... Ahaka yace bby saka rigarki...tatashi tana
mmkn haka....yace ta kwanta tayi barci.washegari bayan
kowa ya hadu a pallow ne aka bude taro da addua sannan
aka aka fito da hjya...samra naganinta ta rugo aguje taxo
tana hjya ina kika shiga ...kafin hjya tabada amsa kande
wato umma tashigo pallow dagudu tana ihu tana kuyi hkri
....can tace nine nan naraba hjya da yaranta....tana mgna
tana xaxxaro ido...tanafadi haka tasoma kuka.
.
Kowa yayi shuru ana sauraronta....can ta fara mgna tana
cewa nice nan nashiga nafeeta naraba hjya da yaranta guda
uku sbda alhji wato baban sadeeq yasamin ido lkcn da aka
auroni shiyasa narabasu ......hjya tamanta tana da yara
guda biyu wato baban alhji da kaninshi wanda yarike
mummyn samra lkcn dana koreta a gda....tana gama mgna
tafara kuka ....itam hjya wato mahaifiyyar ddyn samra da
alhjin sadeeq da kannin shi wanda yarike mummyn
samra....can alhjin sadeeq yayi gyaran murya yace ALLAH
mun gode maka daka nuna mana ranar nan ......can kande
tace dan ALLAH kuyafemin domin yanxun nasani idan
namutu yanxun ALLAH baxai yafe munba....shiyasa naxo
inroki gafaranku gafara......
.
Daddyn samra ya daka mata tsawa yace ke shegiya tashi ki
fita kibamu waje tafara kuka tana dada rokonsu.....alhjin
sadeeq ne yayi gyaran murya yace aa ayafe mata tunda
tariga tatuba....kowa yace yayafe mata sannan aka kulle
taro da addua ....ahanyar komawa gda kande tasamu
hatsari yaxama sanadiyarta....bayan kowa ya natsu ne a
pallow alhji ya kalli samra da sadeeq yace tabbas gasky
mamam adnance wato matar sadeeq tada cewa tabbas
sadeeq yana da dangantaka tsakanib shi da samra ....sbda
tasha kawo min kara cewa ita gasky bata yarda da sadeeq
ba kila samra yar shice bayaso yafada ashe dai gasky ne
kuna da dangantaka ....dandanan pallow ya kaurace da
surutu kowa yana fadin albarkacin bakinsa akan kamanni
samra da abban ta wato sadeeq......
.
Saida kowa yagama mgnar shi akayi shuru sannan hjya
tsohuwa tace samra xo kaima sadeeq kabiyota suna xuwa
kusa da ita ta rungumesu tare tanata samusu albarka tana
cewa in SHAA ALLAHU nan da wata tara xanxo indauki jika
na....yayi maxa ya amsa da ameen itako tasunkuyar da
kanta shiko ya minsileta tayi maxa tadago yamata
murmushi.....bayan taro ya watse kowa yakoma gdan shi
suma su samra ankoma gda...duk tabi tagaji kawai tafada
bayi tayi wanka tana cikin shiri ne yashigo dakin kawai tana
ganinshi taje xata dauko hijabi yayi maxa tarike hijabin
yajawota jikinshi......yace dauko kayanki kixo muje dakina
...
.
Tace abba bara insa kayana yace aa bbyna kixo muje
dakina dashi kisa....tafara xubo da kwalla amma bata bari
yagani ba taje tadauko kayan tayi gaba shikuma yana biye
da ita abaya suna shiga daki yajawo ta jikinshi ya
rungumeta yadago fuskar ta ya manna bakinshi cikin nata
yasoma bata hot kiss......can yace bby xokimun wanka ta
kulle idon ta don kunya ...yayi dariya yawuce bayi ita kuma
tayi maxa tasa kayanta can sai yakirata daga bayi yace xoki
kawomin towel ....ta dauko towel tace gashi abba yace
bude kimikomin tadan bude takawar da fuskan ta tamika
mishi dayaxo amsa yajawo tare da hannun ta....kawai
ganinta tayi acikin bayi gashi ko kaya bai sa ba nan danan
ta kulle idonta da tafin hannunta yajawota jikin ..taji wani
abu na tabata haba ai kawai sai tafafa kyarma.........

Read More »

DAGA DAKIN GIRKI

Girkinki kimarki
Dan farantawa iyalinki tabbata da kin kare kimarki
Download
Read More »

NA MANTA KOMAI Part 5

NA MANTA KOMAI Part 5
.
Na H.M Jabo
.
Yana office amma tunani yake yi, ya zai tunkare ta, ko
kawai yaje ma ta da sunan game d'in ne shi ma? Idan ta ce
ba ta sani ba sai ya gaya mata, dan yana kunyar Mama,
"No I will not do that. Zanje kawai na ce mamanta za ta yi
waya da ita, duk shirmenta ai tasan maman ko?" jeeeem ya
yi, a ranshi ya ce "yarinyar nan fa ba k'aramar shedaniya
bace," tsaki ya ja "zanga dai yanda za ta bullo wa abin, sai
ni ma na san yanda zan bullo ma ta," ya tattara files ya fito,
ya kama hanyar gida yana yan sak'e-sak'e a hanya har ya
isa gida. Palo ya tarar da su ita da 'yar bak'a, ana koya ma
ta girki, dan black duk wani abu na chi to ta na gurin, sabida
tsabar kwad'ayinta, baiko kalle ta ba, ba ta ma san ya shigo
ba, sai ji ta yi ya ce "ki sameni a d'aki yanzux" taji mi ya
fada, haushin ta d'aya kar 'yar bak'a ta ji ta rainata, dan
akwaita da iyayin banza, bayan kamar minti biyar ta mik'e
ta wuce, d'akin ta shiga ta wuce toilet ta wanke
hannuwanta, ta fito da har zata chanza kaya, dan wani
3quarter na Jeans ne a jikinta, sai kuma 'yar figigiyar best,
gata 'yar lukuta da ita, ta tuna a book din nan ance "ba
kullum bane zaka rik'a budewa namiji jiki ba," tsaki tayi
"bayan ya gama gani na ma, miye ya rage wanda bai gani
ba tunda muna da yara har biyu," Turare ta fesa, mai sanyi
sosai, ta bude wardrobe za ta ciro riga sai kawai ta gan shi
ya shigo, ta juyo ta kalleshi, sai ta rufe wardrobe d'in, ta
fuske abinta, da sauri ya kauda kanshi, a ranshi yace "'yar
lukuta kawai amma ta had'u fa , a bayyane ya ce "dama
mama ce takeson magana dake, zaki iya tuna ta?" Gyada
masa kai tayi alamar NO, dariya taso kubce masa sai ya
dake, okay, " mama itace mamarki, gaisheta zakiyi cikin
tarbiya", " ya ake gaisuwa cikin tarbiya?, " ta tambaya,
dariya yayi amma badan yaso ba, dariyar ce taci k'arfinsa,
ya kuwa zauna kamar gaske, ya gaya mata yanda zata ce ,
ita ko harda maimaitawa tayi irin haka kake nufi ko? Gyada
mata kai kawai yayi, a ranshi yace " 'yar rainin wayo kawai,"
ya kira mama bayan sun gaisa yace mama ga autar ki, but
still fushi take dake, ya mik'a mata wayar, tayi d'an gefe da
kan wayar tace dashi "nice auta?" Yace "Eh, " " to kuma kace
na gaidata cikin ladabi, kuma kace mata ina fushi ya zanyi?"
Karbar wayar yayi ya kashe haushi ta bashi sosai, "malama
idan bazakiyi magana ba ki bari! Mahaifiyar kice kike yiwa
wannan shirmen ! Ke idan baki san darajarta ba ni na sani,
kada Allah yasa kiyi mata magana," a fusace ya mik'e, rik'e
masa hannu tayi, a shagwabe tace "kayi hak'uri zanyi
magana da ita kaji" tsaki yayi mara sauti ya dawo ya zauna,
ya fara dannawa, Wait Wait,ta dakatar dashi, " normal zanyi
magana da ita ko kuma cikin fushi? "
.
ya kalleta rai a bace" cikin fushi da ladabi" "yaya kenan?""
ban sani ba " mik'a mata wayar yayi, ta kara a kunne, sun
gaisa fushi fushi take maganar amma da ladabi kamar
yanda oganta ya umurceta, chan mama tace " ga suhail
zaku gaisa " zare ido tayi ta kalli Ahmad, a hankali tace
"waye suhail dan Allah " banza yayi da ita, suhail kuwa yana
chan yana zuba kamar kanya, matsowa tayi daf dashi ta
d'an bubbugashi, waye suhail, baiko motsaba yace "mata
d'an uwanki ne" sannan ta fara masa magana yanata
complain ta sharesu duk fushin ne takeyi dasu har yanzu,
ita kuwa sai aikin bada hak'uri takeyi ba tare da tasan miye
laifin nata ba suka k'are ya baiwa mama, nan mama ta
shiga mata nasiha akan tabi mijinta, ta na ta In sha Allah ba
abinda ta gane sai d'an yak'e da ta ke muvsu ta na cewa
sorry, Mama ba taji dad'in yanda 'yar tata take mata
magana ba, amma tasan su suka mata laifi, sun yi sallama
ta mik'a masa wayarsa " ki ijiye min a nan " ta ijiye har takai
k'ofa za ta fita saita waigo shi, karaf idonsa akanta yana
mata kallon kamar mayunwachin zakin da ya hango nama,
sauri ya yi ya janye idonsa, murmushi ta masa ba tare da
ya gani ba, ta fice abinta, a ranta tace ashe ma har yanzu
yana sona, kawai dan bani da lafiya ne. Chan ta sami 'yar
bak'a ta kusa kammala wa, sorry black na ijiyeki ke kadai..
.
"No ba komai ai kin je gun mijinki ne" kallon ta kawai tayi,
aranta tace "wannan black akwai bala'in shishshigi a gunta,
suka k'are aikin, ta fito zata d'aki kichibis suka yi da shi , "
Sorry " ta fad'a fuska a sake, bai kula taba ya gangara
k'asa ya wuce gun aikinsa.
.
*********
Alhaji Ibrahim ya shirya tafiya wani aiki a morocco, amma
yaga bazai iya tafiya baiga yarshi ba, musamman yanda
take fushi dashi, shiryawa yayi ya kamo hanya, saida ya iso
Abuja sannan ya kira Ahmad ya shaida mishi, yana gari,
Ahmdy cike da farin ciki ya tarbo Dady su ka wuce gida, sun
tarar da Suhaila, 'yar bak'a na koya mata yanda ake sinasir,
gidan ya had'e da k'amshi, Dady cike da farin ciki yau zai
had'u da 'yar autarsa, sunyi sallama, ta fito da sauri jin
maganar Ahmdy da rana tsaka. Sannu da dawowa, ta fad'a
ta kalli mutumin, lokaci d'aya ta gane shi, da yake ta tuna
wasu abubuwan da suka faru lokacin da take 'yar shekara
takwas haka, so ta gane Dady, cikin girmamawa ta
gaidashi, Dady yana ta jin d'ad'i, Ahmdy ya sami gu ya
zauna, a ranshi yace "wato yarinyar nan ta raina min wayo
ko?. Zaki gane Dady d'inki, dama ni nasan duk kissa ce ta
mata" Dady bari na shiga ciki, Ahmad ya barta da Dady
d'inta, nan fa ya fara mata maganar da sam bata san ina ya
nufaba, sai rudar da ita yakeyi yana bata hak'uri, "wai mi
suka min da suke bani hak'ur'i?". Haka ta k'are zaman ta
da rashin sanin kan zance na Dady har sukayi sallama,
Dady zai tafi, ta haura sama ta kira Ahmad sai kuma taji
olooo, dan ba zata iya shiga d'akinsa ba, sai ta dawo, "Dady
ka mishi waya inaga baya gida" "ke Ina wayar ki ?", "ta
b'ace ne Dady ", "ok". Ya kira Ahmad ya sauko suka yi
sallama ya wuce. Za ta haura sama ya janyota da k'arfi
saida ta fad'a jikinshi, " kin raina ma kanki wayo ko? Wato
ni ne baki sani ba, amma kin san iyayenki, miyasa baki iya
playing game ba?", kallon ta ya yi ido cikin ido sai kuma ya
saketa ya juya ya wuce dakinsa tsaye ta yi ta na kallon sa..
.
************
Yau da gobe Suhaila tayi wata daya a gidan Ahmdy, bata
ganinsa sam bare suyi game d'in da ya ke ce wa su yi, duk
tabi ta damu, komai na ta a hankali ta ke yinsa sabida ta
fahimci kamar ta MANTA KOMAI ne, abin duniya ya isheta,
ta yi kuka har ta barwa Allah, tun ta na shiga hanyarsa ya
na disgata har ta daina kula sa, harkar gabanta data
yaranta ta saka gaba, ba abinda ta rasa a gidan komai
normal. Ahmad kuwa a hankali sai yake ganin kamar
abinnan da gaske takeyi, sabida ya aunata a hanyoyi daban-
daban ba tareda ta sani ba kuma ya na ganin lallai kamar
da gaske ta manta komai, sai ya tuna lokacin da "sa" ya
wurgar da ita kanta ya fara bugun k'asa, may be kan ya
sami matsala ne tadan yi missing din wasu abubuwan,
yana son ya kaita asibiti gashi ta d'auke masa k'afa gaba
d'aya, d'an gaidashi da take duk ta daina, duk yabi ya
damu, shima k'arshe ya yanke shawarar zai kaita asibiti
kawai a duba ta. Da wuri ya dawo gida ya tarar da su ita da
yara su na wasan 'yar b'oye idan aka kama mutum shi
kenan, idan ba'a kama shi ba sai aje a goyashi, to kullun in
su ka yi, idan ita ta ci sai su ce 'Dady zai goyata", ana ta
tara goyon har yakai tara. "
.
yeeee Dady zo ka goya Mumy, tana bina bashin goyo hudu,
Rukayyah kuma tana binta biyar, dama munce kai za ka
biya ta," Surayya tace " Mumy zo Dady ya biyaki", "na yafee"
kawai tace musu ta wuce d'akin ta. Tana zaune bakin gado
ta tallabe kumatunta da kanta, sai ta ji shigowarsa, k'in
d'agawo tayi bare tamar magana, yazo kusa da ita, ya dad'e
yana kallon ta, sannan yayi magana "Suhailah, ki shirya
gobe muje hospital a miki check up," kamar bata ji shiba
haka tayi, tayi baya da kanta ta kwanta idonta a rufe, ya
tsura mata ido sosai, har cikin ransa yake jin yasan ta
amma ya kasa tunawa, ya gaji da tsayuwa sai kawai ya
wuce dakinsa, haka ya kwana yana addu'ar Allah yasa
abinda yake tunani bashi bane. Da safee bayan ya k'are
shiri yazo gunta, "ba nace zamu hospital ba?", "Bazan jeba" ,
haka kawai ta fad'a" murmushi yayi "haba maman twins"...
tun kamin ya fadi abinda zai fad'a ta karbeshi, "da gaske
yarana twins ne?", Fuskanta a washe, "idan mun dawo zan
miki bayani", ta turo baki" kaine Dady tun yaushe kasan
bani da lafiya amma kak'i kaini hospital", "kiyi hak'uri yanzu
zamu tafi", haka ya mata wayo ya lallab'a ta suka tafi,
bayan bincike da kwaje kwaje aka gano cewa ta sami
matsala a brain d'inta.
.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.! Hankalinsa ya tashi
matuk'a gashi iyayen ta satin nan zasu zo gunta kuma
zasuyi kwana biyu, tabbas baya son suzo su sameta haka,
za su ga sakacinsa, na rashin kula da lafiyarta, har fiye da
wata daya, kuma duk sanadiyar sa hakan ta faru. Likita ya
tabbatar masa da cewa idan ta sami natsuwa da kwanciyar
hankali a hankali komai zai dawo, daga asibiti direct gun
abokinsa ya wuce ya ce ya masa bucking zai kai madam
waje a dubata....

Read More »

***** SAMRA 5 *****

***** SAMRA 5 *****
.
Washegari duk suka tattara sukayi hanyar kano harda alhji
sumaila da gateman din gdan sadeeq......An taru a pallow
nakasa harda iyayen nafeesat.....Anbude taro da addua
annanne sadeeq yafidi duk abunda yaxo ya tadda aka
tambayi nafeeesat tace ita bata san alhji sumaila ba .....aka
koma kan samra tafadi tun ranar data fara ganinshi har
xuwa jiyan....sannan aka tambayi alhji sumaila yake cewa
shidai shi abokin muamalan tane kuma abkn kasuwancin ta
.....akace wanu irin kasuwanci yace suna siyar da cocaine
ne dasauransu.......yafadee duk abunda yasani......har ila
ga lkcn nafeesat ta musa wai bata sanshi ba....saida
gateman yafara mgna yanacewa tun ranar da captain yayi
tafeeya yakexuwa kuma inyaxo tafeeya sai kin rakashi har
waje....
.
Ahaka dai akacigaba da mgnar stil nafeesat taki yarda sai
da mai gadi yafeeto dawayarshi yabude duka record din
daya dauka lkcn da alhji sumaila yafara xuwa gidan
......yasa ma kowa yaji ana gama ji kowa yarike kanshi sai
alkcn tayarda kuma tace tana dauke da cutar kanjamau
wanda tadau alwashin saita saka ma captain......ananne
captain yace yasaketa saki uku kuma daga nan karta koma
gdan shi aje akwaso mata kayanta........Ahaka dai taro ya
tashi.....Bayan an idda taro ne kowa yagama tafeeya saura
yan gda yakalli tahir yamishi godeeya akan yarike mishi
bbyn shi dakyau ...
.
Alhji ne da hjya xaune asamar kujeran pallow shikuma
sadeeq xaune akasa.....alhji yakalleshi yace gasky banji
dadin sakin dakama wannan yarinyar ba har uku.....sadeeq
yadago yace ayi hkri.......hjya tacr alhji adai mishi mgna
akan yarage xafi amma ai wannan dole yasaketa koda ace
batada cutar ballantana tanada shi......ai dole
asaketa.....ahaka sukayi mishi fada mai ratsa jiki yatashj
yatafee......xai fita kenan daga pallow hjya tace sadeeq
yadawo ya durkusa agabanta......alhji yace yaushe xaku
koma yace gobe in ALLAH yayarda.......hjya tace ai samra
tagama secondary skul koh yace ehn........sai alhji
yakalleshi yace toh...................
.
Xaka barta anan sbda xamuje bikin sistrn ka acan garin
kaduna wato yaryan kannina....kuma inaso kamu kaima
xaka xo kadunan so dat u can attnd d weddin.....yace abba
bakomai duk yanda kukayi da ita itama yarkuce... ..suka ce
ALLAH yamaka albarka yace ameen yatashi yatafee......wa
she gari suka shirya xasu tafee bby tanata kuka xata rabu
da ddynta .....taje tarungumeshi ta abba yanxun shekara
nawa xaka kuma yi....kowa yana darya yace ranar fridy
xan dawo tace toh ALLAH yakiyaye hanya ya amsa da
ameen sun shiga mota xasu tafee takuma xuwa tace abba
ka tabbata bawani tafeeya xaka kuma ba.....yace toh bby
nataba miki karya ne wai tace aa amma kamin alkawari
xaka dawo ranar friday .......nayi miki alkawari
toh.....ahaka suka wuce yana kewar bbyn shi......itama
tana kewar shi amma dataga bby adnan akusa da ita sai
yadan ragu ...
.
Ranar friday dasassafe samra tashiga kitchen don yima
ddyn ta girki na tarbonshi......haka koh tayi mishi haddaden
dishes yanaxuwa yaci yanata santi.....suka kama hanyar
kaduna don xuwa biki kuma aranar xaa sama fatee kanwar
sadeeq rana a can kadunan sun isa kaduna lfy.....bayan
daurin aure aka saka ranar bikin fatee nanda wata biyu.....
.
can aka aiki samra cewa taje takira wata mata daga daki
tace ita batasan dakin ba.....kunsan waye kanin alhji dake
kd dasuka xo bikin yarshi bawani bane illa wanda yarike
mummyn samra tunda tafeeto gda kuma yanxun ma itace
akace taje takira tace bata san dakinba.....sbda kannin ddy
yabama su alhji labari shine suka ce akirata....ananne
akacema fatee taje takirata .....suna xuwa kirjin samra
yafara duka .....suna shigowa pallow da fatee kowa
yakaiduban shi ga ita....samra na daga ido kawai sukayi
toxali da mummyn ta .........tasaka hannu tana pointin dinta
amma takasa mgna itama dai haka mummy take pointin
dinta kawai sai su bi yun suka xube akasa...... Kowa sai
kallon juna sukeyi can sadeeq yatashi dagudu yaje yadago
bby.....kowa ma yataso dakyar aka samu damar ceto
rayuwansu ......sai da duk suka farfado tukun mummy
takalli samra tace samra ina kika shiga itama kusan haka
samra ta tambayi mummy can suka fashe da kuka dukan
su adaidai wannan lkcn ne wani abokin kanni alhji yashigo
yana cewa lfy kowa yadago yakalleshi haba dandannan
samra da mummy suka hada baki suka ce ddy....kowa sai
kallon su yake da mamaki.....kunsan waye wannan
mutumin.......... Daddyn samra ne yashigo kuma shine suka
gani kawai xubewa yayi akasa yama kasa mgna itakuma
samra xama tayi akan cinyar abban ta .......kawai tafashe
da kuka ananne alhji ya yi gyaran murya kowa yadago
yakalleshi yabude gurin da adua......sannan kowa yafara
fadan albarkacin bakinshi bayan kowa yagama fadin abinda
yafaru abaya.....Daddyn samra yayi masu alhji da kanni shi
godeeya yasanar musu cewa kande daga baya taxo
tahaukace kuma tafadee duk abunda yafaru .....sannan
yace waye wancan samra tago taga da abbanta yake mgna
.....alhji ne yace shine dana na farko kuma shine yarike
samra tuntana karama harta girma....
.
Daddyn samra yace toh shidai yagode sosai yace kuma
yabarwa alhji samra hartayi aure sai dai inta samu hutu ta
iya xuwa tagaida su ananne yan biyun mummy suka je suka
rungume samra da daddyn su ......bayan haka akayi kulle
taro da addua .....bayan ankai amarya dakinta ne daddyn
samra yakira alhji da sadeeq gafe yace yabawa sadeeq
auren yar sa har abada kuma xaiso ahada auren nasu da
na fatee kanwar sadeeq ......ananne alhji yayima daddyn
samra godeeya ......
.
Washegari daddy yadauki mummy da yan biyu suka koma
gda ......suma su sadeeq aka koma gun aiki yanats murna
shima alhji yasanar da hjya tanata murnar wannan
hadin....amma sunki su sanar da samra sbda sunsan
baxata ji dadi ba....har ita fatee baa sanar mata ba don sun
san xata iya fada mata.....Bayan wata daya da sati biyu
aka fara shirye shiryen biki itadai samra tanatama fatee
darya wai xatayi aure .....amma abunda ke bata mmk shine
duk abunda akama fatee itama sai anmata ....... :
.
Amma duk da haka bata kawo komai aranta ba....amma
xuwa lkcn fatee tasani ....aranar daurin aure ne bayan
mummyn samra ta iso rakirata daki tafada mata duk
abunda ke faruwa ananne tasaki kuka kamar ranta xai
fito......bayan andaura auren fatee da muktar sannan aka
daura na samra da sadeeq......annane maroka suka fara
ihu suna andaura auren fateema da muktar sannan na
samra da......bata bari ankarisa ba tatoshe kunnenta domin
har lkcn bata san waxata aura ba kuma batason
tasani........bayan taga gdan yadanyi sarari ne tadauki
takalminta tatafee sbon gdan da abban ta yagina kusa da
gda.....tahir ne yafara hango ta yace gafa amarya nan
xuwa haba dan danan yaje yatarota tasakin mai
kuka...........

Read More »

movies series

The originals S04E02
Download
Read More »

HAUSA HIP HOP

B. O. C Yawo
Dan nishadantarwa domin download
Danna wagga
Read More »

GIRKINKI KIMARKI

Tabbatar da kimarki domin qayatar da iyalinki
Danna nan
Read More »

NA MANTA KOMAI Part 4

NA MANTA KOMAI Part 4
.
Haka take bacci a palo tana jiran mijinta, sai dai ta farka ta
ganta a d'akinta, tare da yaranta yau kwana biyu kenan.
Cikin dare ta farka ta kasa bacci ta tashi ta zauna, tana ta
kama tasha, ta dai rasa abunda ke mata dad'i, ta rasa gane
kan komai "to wai haka ake aure dama?" tambayar da ke ta
yi mata yawo ke nan cikin kanta, ta k'ara d'auko d'an littafin
nan data gani a kayanta ta k'ara karantawa, taga yanda ake
soyayyyah ake tarbar miji, a masa girki, kwalliya, uwa uba
kwanciya, amma ita ko k'eyarshi bata gani bare ta mishi
wani abu, a zuciyarta ta na ganin hadda laifinta, da take
bacci da wuri, kuma take tashi letti, dole ta dage ta rik'a
jiranshi har ya dawo komin tsawon dare, amma ace baka
magana da miji, ko ganinsa ma bakayi ta na ganin kamar
hakan ba dai dai bane,. Kodai akwai wani abu da bata sani
ba bayan wanda aka rubuta a littafin? Wata zuciyar ta raya
mata ta kwashi yaranta yau su kwana a dakin shi kawai,
amma kuma sai ta fasa, "to wai dama haka muke dashi, ni
kuma miyasa bana iya tuna komai ne? Mi yake shirin
faruwa dani ne? Kamar akwai abinda ya faru amma na kasa
tuna komai WAI MA YA SUNANA?" A haka tayi ta tunaninta
ta k'are tayi kukanta sannan bacci yayi gaba da ita. A haka
sai da Suhaila tayi sati d'aya bata ga mijinta ba, kullun itace
hidima da yaranta, gashi wani sonsu ta ke ji a ranta kamar
me, ta saba da su kamar hauka. Rannar da gari ya waye
suka shirya kamar kullun sai Surayya ta kama hannunta
tace "Mumy miyasa bakya son kaka Rabi?"
.
A ranta tace waye kaka Rabi kuma?" Ta tambaya, " To yau
kizo muje ki gaishe da, kullum ita take gaya mana ranar da
zakizo har kikazo, ko bakya sonta ne? Rukayyah ta
tambaya" da sauri Suhaila ta gyada kai, "ina sonta mana,
nama fiku sonta" oya muje ku rakani, "amma ku tsaya, a
cikinku wa zai gaya min idan naje gaidata da safe ya nake
ce mata?" Yaran suka kalli juna, suna murmushi su kace
"Mumy ai baki taba zuwa gurinta ba" nan ma kanta ya k'ara
kullewa, a ranta tace" ban taba zuwa gurinta ba? To ko bata
dad'e gidannan ba" yamutsa fuska tayi ta basar, "oya to ku
zo muje" ta rik'e hannun ko wacce suka tafi gun kaka Rabi.
Da yake sassan gidanta daban yake amma a jikin babban
gidan gonar ne, dan tace ita bata son bene, ina ruwan yar
tsohuwa Rabis. Suna shiga suka ruga suka rungumeta suna
kaka Rabi oyoyo suna dariya, tace "ni dai to kuyi a hankali
dai karku k'arasa ni kun sami Momy kun manta da kaka
ko?" ta fada tare da rungumesu, tana "fadin lale marhabin
da Momy, tare kuka zo? Shigo ciki mana keda gidanki,
bisimilla zauna ga kujera nan" haka kurum sai Suhailah taji
tana jin kunyar kaka Rabi, a ranta kuwa sai sak'e-sak'e
takeyi, "ko waye wannan kuma oho?"
.
Tunda tazo take jin sunanta, tama taba hangota sau d'aya
amma bata tab'a ganinta ba sai yau, sai kame kame take
sabida kayan jikinta, Kamar dai ya dace ace tasa kayan
traditional irin na jikin kaka Rabi, "to waima in dai nan take
zaune ai ya kamata ace ta tab'a zuwa gaisheta, kai tabbas
akwai wani abunda bata sani ba, to menene wannan abun?"
Dama ba wando da riga ta saba, ta mayar dasu kayanta
koda yaushe su take sawa, tsaki tayi a ranta tace "da ba
tazo dasuba, tun da dai tana kyautata zaton uwar mijinta ce
tunda 'ya'yanta suke ce mata kaka, " nikam na shiga uku,
na kasa gane komai! Ko mijin nawa ina yake oho? Kamar ta
tambayi kaka ina yake, sai ta tuna a littafin da ta karanta
ance a rik'a boye sirrin miji, wannan ma sirri ne sai ta fasa.
Haka ta zauna ta gaisheta cikin ladabi, "kaka tace Suhailah
ya jikin naki,kin samu sauk'i ko?" nan take gabanta ya fadi,
"ashe bani da lafiya ma?" Ta cigaba "Ahmad yace min kin
fadi ne baki ji dadi ba" shiyasa ma baki zo ba, kuma nace
zan lek'oki yace wai kina jin kunya ne da kin wartsake zaki
shigo, shi yasa baki ganni ba nima, jikin da sauk'i ko?" tayi
murmushi ta rufe fuska, cikin jin kunya tace "eh da sauk'i
sosai," ta dad'e a duk'e dago kan da zata yi sai taga kaka ta
d'auki waya ta kara a kunne tana magana, tashi tayi da
sauri ta fita, kaka tayi murmushi "ko ta d'auka sirri zanyi
yarinya mai kunya" Suhaila kuwa tana tafe tana sak'e sak'e,
lallai bata da lafiya, shi yasa take jinta kamar ba itaba, ta
tuna ko sunanta ta manta, idanuwanta suka cika da kwalla
ta shiga d'akinta ta k'ara bincike yan kayan da ke cikin
jakunkunanta biyu, nan ma bata ga komai ba da zai sa ta
tuna wani abu, ta k'ara bubbud'e duk wani wuri da take
tunanin zata ga wani abu sam bata ga komai ba, anan ta
k'ara fashewa da kuka, kuka sosai take har da sheshsheka,
to me ya Sameta?
.
Tana nan zaune tana kukanta taji yaranta na hawowa sama,
suna ta surutu, tayi sauri ta goge fuskarta, kamar zata
shige bayi ta wanke fuska, sai ta fasa, koda suka shigo tare
da Dady suka shigo, shima bata san sunanshi ba, in ba dan
taji kaka Rabi ta fada ba, idanunta suka k'ara cika da kwalla
ta mike tsaye, taso taje ta rungume shi, kamar yanda ta
gani a littafin data karanta, (kada yara su hanaka yiwa
mijinka soyayya) amma ta kasa, sai kawai tace "sannu da
zuwa" ya kalleta a karon farko tun bayan zuwanta gidanshi,
sabida a palo ma idan ya ganta tayi bacci d'aukar ta kawai
yakeyi ya kaita d'aki ya shinfidar dama wutar palo a kashe
take, baya wani kallon ta, gata da nauyi kuwa, amma haka
yake tallabota ya kawo daki, ta k'ara ramewa, ga idonta
cike da kwalla yayi jajir dashi, murmushi kawai yayi, a
ranshi yace "zaki k'are felek'en ki ne yarinya" amma da
mamaki wacce yaji labarinta shez always happy and active,
amma yanzu duk ta canja cikin sati d'aya, idan ma
saukowa tayi ai ya dace ta kawo kanta ne kawai, bawai ta
tsaya jan aji ba. Ya amsa ta sama sama "yauwa sannunki "
Matsowa tayi maimakon ta rungume mijin sai ta rungume
yaranta "Mumy wa ya dakeki kike kuka? Ko kaka Rabi ce?"
Tace, " no abune ya shige min ido yanzu, amma na hureshi"
ta dago ta kalli mijinta a karon farko bayan sati d'aya,
kamewa yayi, yace" kunga na kawoku gunta dama wasu
files nazo dauka, bye d'inku" suna murmushi suka d'aga
mai hannu "bye Da88dy" ya juya zai fita kenan tace "ina son
magana da kai" ya juyo ya kalleta, sai kuma ya cigaba da
tafiya sai da yakai k'ofa har ya fice sanan " yace ina zuwa"
.
Fitarshi da kamar minti biyar Nanny dinsu Auntie 'yar bak'a
tazo ta lallabasu, da k'yar suka yarda suka bar ta, 'yar
bak'a ta tafi dasu dan tayi masu wanka da shirin bacci
dama dare yayi, ga dukkan alamu Ahmad shi ya turo ta.
Fitarsu da kusan minti goma, sai ga Ahmad ya shigo d'akin
cikin k'ananan kaya bak'in wando da farar shirt, duk da
hankalinta a tashe yake, dan jinta take a rude, a ranta ta
yaba da shigarshi, da alama daga wanka ya fito, sai
k'amshi yake, ta dago kai ta dube shi tayi mashi murmushi
wanda ya kasa gane mi yake nufi, sai ya basar dai-dai
lokacin da yake shirin zama saman wata kujera da ya jawo
daga gaban mirror ya kawota gab da bakin gado kusa da
inda take zaune ya zauna, ya k'ura mata fararen idonsa,
bakinshi kamar ya shafa lipstick sai maik'o yake, sai ya
burgeta har cikin ranta, yace "miye maganarki?" yana tsotsa
minti a hankali, ta kauda kanta daga dubanshi ta tunzuro
baki kadan, wai ita ala dole shagwaba, dan a littafin data
karanta ance shagwaba tana sanya mace ta saye zuciyar
mijinta lokaci daya,namiji zai ga yanda kika k'ask'antar da
kanki gabanshi kina harkar yara, bare kuma shi dama namiji
kamar rak'umi yake a gun mace, idan baki iya sarrafashi ba
to kuwa zai zame miki kamar ingarmar doki da zai zo yafi
k'arfinki, dole sai ana hadawa da shagwaba da lallabawa, a
book din an kawo misalin yanda za'a rik'e miji a nuna mishi
fushi, ba wai da daure fuska da kunbure kunbure ba, da su
gaba ba, no da kissa da kisisina irin ta mata, an kawo
misalan yanda ake yiwa miji shagwaba da tasirin shagwaba
a gun miji, wanda sune Suhailah take jarrabawa. A sanyaye
a shagwabe take maganar, tace "nasan bani da lafiya,
amma ya kamata ai kayi mani bayani," yanda ta mishi
magana cikin sanyin murya, da yanda ta shagwabe masa
ya burgeshi, wanda yake ganin kamar gaba d'aya ta sauko
ta barwa Rabbana komai. Yace "wane irin bayani zan miki
kuma? Bayan kin san baki da lafiya mi zan miki?" Ido ta
dago ta mai wani kallof,, saida yawu suka sark'eshi, saida
yayi guntun tari, a ranshi yace "wato yarinyar nan ba
k'aramar 'yar rainin hankali bace" duk suka yi shiru na wani
lokaci sanna ta cigaba da cewa, "dama haka muke zama
tuntuni baka zama gida? Kuma bama magana?" Dariya yayi
sosai, ya kalleta, sama har k'asa ya girgiza kansa, sai kuma
ya d'aure "Please kada ki nemi ki bata min lokacina, inada
ayyukan da ya dace nayi, idan kin hada wani plan sai ki
nemo ni, but now, game is over for you" ya mik'e zai wuce
da sauri ta rik'e hannunsa, sokoko yayi yana kallon ta, ta
zaunar dashi ya kuwa zauna. "Zan maka tambaya uku
zuwa biyar duk lokacin da kake free sai ka bani amsa" "
.
please wacece ni? Miye sunana? Ina iyayena? Kuma inane
naje da yarana suke murnar dawowata?" Ta kalleshi sosai,
taci gaba "nifa ba abinda na sani a kan kaina, bare wani
nawa kai kanka ban san sunanka ba, amma nasan kai
mijina ne, tunda ga yaranmu nan da nake tunanin yan biyu
ne, suma da ace banga gashin kaina da nasu iri daya bane
wallhy da nace ba yaran mu bane, dan Allah duk lokacin da
kayi free ina jiran amsoshi na" ta mik'e da sauri zata nufi
hanyar bayi, dan kuka na neman subuce mata, rik'o hannun
ta yayi ya juyo fuskarta suka fuskanci juna "Thank God da
kika san cewa I am your husband, yanda kika gane cewa ni
mijinki ne, wannan ma ya zame miki assignment kije ki
gane amsar sauran tambayoyin ki" ya nunata da
hannu,"shame on u da kika yi failing game dinki ranar farko,
kin kasa winning duk zamanki smart girl," sauke kafada
yayi, but still you try, u can go on, may be next episode u
can win, but now u fail Zeroooo" ya fadi zero din yana zare
ido, yanzu muna 1-0. Ya kalleta kallon kinyi missing yace,
"zaki zama fa gud player but u need more & more training"
tsaye tayi tana kallon sa, gabaki daya ya k'ara batar da ita,
ya k'ara dagula mata lissafi, ya k'ara sata wani duhu bayan
wanda take ciki, ta yanda bata ma san ta inda zata kamo
lamarin ba. "kina iya wucewarki, ina jiran next episode" ya
fada yana murmushi juyawa yayi ya wuce abinshi, har ya
kai bakin k'ofa sai kuma ya tsaya yace "idan kin shirya wani
din ina d'aki na ki kirani, da kin bi nan corridor direct zai
kaiki d'aki na, dan nasan shima zaki ce baki san gurin ba"
ya juyo da kanshi da kafad'arshi ya kalleta, idan kuma kin
yarda game is over duka d'aya ne a gurina, ya wuce abin
shi duk da bata san ina zancen shi ya nufa ba ta sami kanta
da bashi amsa da cewa, "d game is not over, yanxu aka
fara ma" da k'arfi ta fad'a ta yanda zai jiyota. Murmushi
kawai yayi ya wuce abinshi, ya shiga d'aki yana tunanin
wannan yarinya, tama raina ma kanta wayo, dan ba shi ta
rainawa wayo ba, ya cije yatsa, ya naushi iska, "miyasa ban
biye mata bama? Da sai na bata amsa kamar yanda ta
buk'ata, dan kuwa zata yi dadin playing, dan zan ta winning
dinta ne, ko ba komai she's beautiful & she make me happy
today, in fact she make my day, kan gado ya fad'a yana ta
tunanin Suhaila da abinda ta mishi, yana ta murmushi,
mata akwai fi'ili, yana ganin fuskarta kamar ya santa,
musamman lokacin da ta mishi wannan shagwabar tata,
amma ya kasa tuno ina yasan ta, shi duk ya d'auka da
gaske game take dashi. Bai san seriously Suhaila tayi
loosing memory dinta bane.
.
********
Can gidan su Suhaila kuwa da suka jita shiru, sai suka yi
tunanin ko har yanzu bata huce bane game da irin auren da
akai mata, tunda ta nuna bata so, k'arshe ma tak'i bari
akaita ne, tayi fushi dasu, dan haka yasa ta kashe wayar ta,
dan duk wanda ya buga baya samunta, idan aka tambayi
Ahmad sai yace tana nan lafiya lau, mama ce ta damu akan
sai tayi waya da autarta, ta kuwa dami Ahmad akan ya kira
ya bata suyi magana! Ya kenan?

Read More »

***** SAMRA 4 *****

***** SAMRA 4 *****
.
Bayan kwana biyu da dawowar samra daga skul taraka
abbanta gidan tahir......matar tahir dai mutuniyar arzikice
suna xuwa taje tarungumeta tana murna.....wayyo tace
bbyn abbanta y gda ....wato kin dawo daga skul ko kixo
gdana koh ai babu komai....tahir yace kyaleta aifada
mukeyi da ita bata son xuwa gdan mutane daxaran abbanta
nagida tagwammace tayita xuba mishi shagwaba....takalli
abbanta tace abba kagansu koh...yace barsu kawai xanyi
mgninta...ananne matar tahir takalli abba tace sadeeq wlhy
bakaramin kama kukeyi da samra ba...sukayi darya sai taja
samra zuwa kicin suka cigaba da girka abincin.....bayan
sungama takalli anty wato matar tahir tace ina balain son
iniya girki amma babu mai koyamin amma xanma abba
mgna akan indunga xuwa nan ina koya haka suka cigaba
da fira har suka fito kicin aka fara cin abinci......bayan
angama ci ne taje taxauna akan kafar abbanta kamar wata
karamar yarinya fa mutuniyar da yanxun she ix 15.....tace
abba inso indunga xuwa wajen anty inakoyon abinci kafin
mukoma skul....yakalleta yace bakomai....can yace bby
kinkara nauyi haba ai nandanan tafara kukan shagwaba
suko tahir da matar shi sakin baki sukayi galalal suna kallon
ikon ALLAH...
.
Sai wajajen karfe 5pm suka bar gdan ....suna barin gdan
basu xame ko ina ba sai wani super market da ake siyar da
fone ....anne yace taxabi kowanne...tace abba ni yace ehm
kixaba nace anne taxabi wani wayan yabiya suka xame
inda ake siyar da gold sace taxaba namma taxaba olmst
200000thousand ahaka yaje A T M yaxari kudi yabiya suka
xarce inda akw siyar da kaya suka siya kaya masu yawa
sannan suka koma gda.....Da daddare yashigo dakinta
yaxauna akan gado yarike mata hannu yace bby wannan
gold din kirikeshi da kyau kije kiboye shi tace toh abba ngde
tanata mishi godeeya tare da aduoi yaji dadi sosai anne
suka cigaba da hira har tafara jin barci sannan yatashi ya
jamata kofan dakin ta yawuce nashi yanashiga yaga
nafeesat abikin gadonshi da wasu kayan barci shara shara
yakawar da kanshi ya neman tsari daga shaidan...... tataso
tanata wani yauki kaxo tahau ruwan cikin shi hankalin shi
yabi yatashi....shikuma sadeeq bawai don komai bane
yakesawa baya sonta ila sbda yasan duk halinta na bin
bokaye dakuma bin maxa amma ita stil bata san yasani
ba....duk da tanada aure bata bar xuwa wajen kwartayenta
ba.....haka yasa yatsane ta...amma ayau bayanda ya iya
dole yabiye mata don tagama dashi ....ahaka dai suka raya
wannan daren ita atunaninta da mgnin da boka yabata
yafara aikine....itakoba wai don komai bane takeson sa
sbda ya iya xxx sosai ne.....su nafeesat manya....
.
Akwana tashi bawuya wajen ALLAH yau samra anshiga aji
na biyu adaidai lkcn ne bikin anty sadeeya tatashi daidai
lkcn ne kuma abban ta xai tafee course nashakara biyu
......sai dasuka tafeene takira wani mlminsu a skul dinsu
yace abata fone suyi mgna ananne yake fada mata cewa
yatafi course na 2 yrs haba ai nan da nan tafara kuka
dakyar yasamu ya lallabeta yace xaaxa adauketa daga gda
sbda bikin anty sadeeya da hafsat yakuma yin mata
alkawarin kiranta kodayaushe ahaka dai suka rabu...
.
Bayan bikin su sadeeya ne aka dawo da ita
mkrnta...AKWANA atashi su anty nafeesat an haifo yaro tas
kamar samra komai nasu iridaya alkcn da yaron yayi 3
month tafara fita wayon duniya sai tafeeta taje takwana a
gdan samarinta adaidai lkcn ne tafara rashin lfy tadau
alwashin saita shafama sadeeq cutar kanjamau don dataje
assibiti aka cemata tana dauke ne dacutar HIV......duk
dahaka bata bar bin maxaba ....bayan wata daya
dafaruwan haka ne tasamo wata tsohuwa wanda xata
dunga kulan mata da da koda taje yawonta bata dawo
ba....itako antynta tun asali bata bata abinci inhar tadawo
gda hutu ko taje gdan tahir tacu koh kuma ta girka da kanta
sbda alokcn taxama expect wajen girki ahaka dai takarike
hutun ta tare da tunanin ina antyn ta takd xuwa dabata
kwana a gda .....amma kuma kodayaushe suna manne da
abbanta acikin waya.
.
Ranar mondy ne su samra aka gama final exams nabarin
mkrnta........Ranar samra tayi kuka akan rashin ganin
abbanta haka driver ali yaxo daukanta tamayar da ita gda
batare da antyn ta tasan xata dawo ba.....don ko driver ali
captain nd yakirashi yace yaje yadauko ta......tana dawowa
yashiga pallow ta tarad da antyn ta da wani mutum taje ta
gaidashi ita atuna ninta dam uwan anty ta .......tana shiga
daki tafito kuma da gudu tana boi boi wato adnan kenan
dandan sadeeq wato abbanta yana jin muryanta yafito da
gudu yana mata gwaranci suka rungume juna suna murna
.....shiko bakon anty wato kwartonta alhji sumaila yanata
kallon samra kamar wani maye dayake alokcn samra
taxama wata kakkyawar yarinya idan kaganta saikayi burin
ka kara kallonta.....
.
Yajuya gun nafeesat yace wacece wacan yarinyan.....ta
tabe fuska tace kanwar mai gdana ne yace yaxaayi
inshigeta tatabe fuska tace karkadamu xuwa gobe kadawo
tana mgna tanata washr baki don alhji sumaila yanada
kanjamau kuma tanason ya bata rayuwan samra sbda ta
tsaneta.....Washegari misalin karfe 10 nasafe saiga alhji
nan a gdan kuma aranar ne captain xai dawo alkcn ma ya
shigo abja yana gab da gida amma sai yaji xuciyar shi na
duka sosai.....kawai sai yakara ma motan wuta yanata
gudu don yakosa yaje gda yaga bbyn shi kuma yafiso yaxo
suprisly to evry 1.......suko acan har nafeesat takira samra
tace taje anason mgna da ita kawai tadauko hijabi tasaka
ashiga dakin da sallama yana ganinta yafara
murmushi....kawai sai yafaki idon ta yasa ma kofan key
amma yamanta baisama kofar waje key ba .....yana
gamawa yafara matsowa kusa da ita ...itako sai matsawa
baya takeyi..... Tana lfy mallam anty tacemin kanaso kamin
mgna kuma meye na matsowa kusa dani ....budar bakinshi
yace aiwannan shine mgnar kawai daidai lkcn ne yacafko ta
yawurgata kan gado yarike hjbin ya yaga shi biyu yarage
vest din datasaka kawai da bra sai wando....tafara ihu tana
kiran anty itaku nafeesat sai shewa takeyi akan gado tana
aikin gama yagama daidai wannan lkcn sadeeq yashigo
pallown shi yaji ihun bbyn shi yayi maxa yaje kofar dakin
yadauki spear key yabude dakin shiko alhji har yayi kokarin
rabata da vest dinta daga ita sai farar bra kawai yana bude
kofa yaga abunda ke shirin faruwa kawai ya ture alhji
sumaila xuwa bango yayi maxa yacire kakinshi nakai ya
bawa samra tasaka yayi maxa yakira security men na gate
akan kar subar kowa yafeeta daga gdan inba shiba shiko
alhji najin haka yafara rokon sadeeq amma wani
mahaukacin mari captain yasakar mishi yasashi yin
shuru.........
.
Haka captain yayi ta jibgar shi kamar yaga kayan wanki
itako samra sai rokon shi yake akan yabarshi amma
ina....itako nafeesat tanata murna can tafara jin ihun alhji
ada taxata dadi ne yasashi ihu amma dataji abin ya sananta
yasatw fitowa dga daki domin taxo ta duba tana budewa
tagw sadeeq tayi ihu......ta hau ja dabaya dabaya amma
kafin tafeeta yakamota yasakata acikin wani daki yakulle
......kawai yakoma kan alhji yaci gaba da dukanshi......i
tako samra baiwar ALLAH dataga abin bana karewa bane
kawai tafeeta taje gdan tahir tako ci saa yana nan
....taxaiyyana mishi komai haba ai dan danan taja shi sai
gda.......
.
Suna isa gda suka shiga daki suka samu still bai bar
dukanshi ba har jini ya fara fita daga hancin alhji....dakyar
tahir ya kwaci alhji sumaila daga gun sadeeq .....yana ganin
an amsheshi yafita daga dakin shi yaje yadauko bindiga
daga cupboard yanufi dakin daya kulle nafeesat ........tana
ganinshi tafara kyarma yace kifada min gasky ko in kasheki
tafara fada mai duk abunda ya faru ......dai dai lkcn tahir
yadamu alhji ya farfado yahau neman sadeeq acikin gdan
yaxo wucewa tawata daki yaji kamar mgnar nafeesat
yabude daki yashiga yaxauna shima.....sai data gama
mgnar tukun sannan tahir yatashi yaje yadauki alhji sai
assibity......ananne sadeeq yakira abban shi yasanar dashi
komai ......abba yace duk su tattara suxo gobe harda iyalen
tahir dashi kanshi tahir.......

Read More »

GIRKINKI KIMARKI

DAN FARANTAWA IYALINKI KIKARE KIMARKI

download

DOWNLOAD
Read More »

***** SAMRA 3 *****

***** SAMRA 3 *****
.
Bayan kwana 2 da samra tafada ma sadeeq mgnar
karatunta yasamo mata lesson teacher yana koya mata
krtun a gda harda malamin isalamiyya.....taji dadi sosai
shikuma yayi hakane don kar kowa yaganta a gdan
shi.....wata ranar captain yafita wajen aiki da wuri kuma
fone dinshi akashe yake.....shikuma tahir yanata kiran
wayan shi baya shiga kawai yace bara yaxo gda....aikuwa
yanaxuwa gda yatura kofa kawai yaganta a pallow tana
assignment dinta ya tsaya na kallonta yana mmkin irin
kamanni dake tsakaninta da sadeeq.....yake ke wacce
takalle shi tace samra ce.....daidai lkcn ne captain sadeeq
yadawo daga office sbda wani ciwon kan dake damunshi.
.
Yana shigowa yagan motar tahir a tsakar gida....kawai
hanjin cikin shi ya kada...dakyar yashiga pallow ya tadda su
a pallow yana shiga tahir ya kalleshi yace sadeeq waye
wannan yarinyar yace kabiyo ni daki.....itako tace abba
sannu daxuwa yace yauwa bby tace meyasa naganka haka
yau yace kaina ne keciwo dan danan idanunta yayi raurau
xatayi kuka......yace aa bby bance kiyi kuka ba ai naji sauki
tace toh abba kayi drya kawai sai ya tunsure da drya sbda
yanda tayi mgnar....shiko sadeeq yama manta da wani
tahir a gun shiko tahir sakin bakinshi galala yana kallon ikon
ALLAH don yasan sadeeq bamai yawan son mgna
bane....ballantana kuma wani drya ko murmushi da kyar
yakeyi ballantana drya.....bayan yagama ne da bbyn shi
yajuya yace ooo sry tahir xomuje....tahir yana tafeeya
amma yana tunanin yaushe tahir ya haihu don yaji tace wai
abba can kuma yace aa ba yarsa bace kwartuwan shice
haka dai yayi ta tunani har yashiga cikin dakin sadeeq........
.
.
Suna shiga cikin daki yaxauna yace tahir kar ka xargeni da
komai...anan ne yabama tahir lbrn komai....tahir yanuna
shidai bai yarda ba...yace tunda dai kanuna rashin
amincewarka xomuje ka gani da kanka amma kaine xaka
tambayeta kuma ka tabbatar kayi mata tsawa sbda ta
tsorata tayi mgna amma ni baxan xauna a gun ba.....yace
yaji aikuwa suka fito tare xuwa pallow captain yabi hanyar
fita shiko tahir yakalleta yace inane gidanku ina mamanki
da babanki......dayaga batada niyar mgna sai ya daka
mata tsawa ta tsorata tabuda baki xatayi mgna kenan
tafadee kasa nan danan captain yarude yaki sadeeq akaxo
aka dauke ta xuwa daki sadeeq ya yayyafa mata ruwa
tatashi......tashige jikin sadeeq sai barci yadauke....shiko
captain tahir yace amma sadeeq wlhy kuna kama da
yarinyan nan....amma natausaya mata....nan dai suka
cigaba da tattaunawa ynda xasu taimaka mata..........
Bayan 1yr...aka tsoma shirye shiryen bikin tahir annanne
hankalin sadeeq yatashi don yasan iyayenshi xasu xo kuma
baxai so haka ba....amma bayanda ya iya ya barwa ALLAH
lamarinsa.....ranar frdy kowa ya iso harda kanninshi duka
....suna xuwa suka ga samra alhji da hjya sunata kallonta
sunyi mamaki sosai sbda kamannin su daya da
sadeeq....suka ce ke xonan ke wacece tace ni yar abbace
suka ce wani abba tace abba abba dai ....sukace tatafi
suka xauna jiran dawowar sadeeq......yana isowa yaje ya
gaida iyyayen shi suka ce wacece wancan .....yafada musu
komai suka ce basu yarda ba suka ce akirata annanne aka
kirata ......suka mata tambayoyi kamar yanda tahir yamata
amma kawai tsintarta kawai suka yi akasa.....
.
Ananne yasu yi masa fada akan rashin fada masu dabaiyi
da wuriba.....kuma abba yasanar da shi yamishi mata wato
NAFEESAT...nafeesat dai ba mutumiyar kirki bace gata yar
iska nakarkee ...kuma alhji yace mishi ya tsayarda ranar
bikin bayan na tahir da wata 2 haka yatashu jikin shi duk
yayi sanyi......yashiga cikin gda ya tadda fateema tar autar
su da samra anata wasa....tace abba oyoyo yace ku shirya
anjima inkaiku shan ice cream.....tace yeh taje ta rungume
abbanta....yafeeta annanne suka yi karo da nafeesat tana
ganinshi tafara wani yauki shiko kamar yashaketa sbda
haushinta yakeji... Yakalleta yace matsamin inwuce....tace
haba sadeeq bamu gaisa ba fa....tawani narke yace to
sannu tace kadai ji abunda ddy yace koh nasan kayi farin
ciki kamar yanda nima nayi farinciki..ya kalleta yace sannu
toh.........Ranar saturday aka daura aure tsakanin tahir da
bilkisu.....aure wanda ya tara dumbin jamaa....hmmm
bayan daurin aure ne alhaji da hjya suka kira sadeeq da
tahir akan mgnar samra wai sunaso anemi malami yaduba
samra kafin su tafi ....sadeeq yayi murna sosai yayi ma
iyayen shi godeeya tare da tashi .....ahaka suka tsayar da
akira mallamin washegarin rannar daurin aure....
.
Bayan mallam yaxauna yabude taro da addua yace yana
bukatar ruwan xam xam da dabino......aka kawo mishi
yace ina samra take ta makalle ma abban ta....tace abba
yace bby tashi kije....tana xuwa yakama kanta yafara tofa
mata addu'oi tafara sandarewa tana ihu yadauki yani garin
mgni ya shaka mata a hanci ya saka wani uban kara tana
neman hanyar guduwa yadauko lobari ya kama kafarta
dashi.....yace baxakayi mgna ba.....yafara ihu shiko
malamin yadunga watsa mata ruwan xamxam dayayi krtu
aciki.....yasoma xanyi xanyi yace toh kai waye yace
dafarko dai aikoni akayi domin inshiga tsakanin ta da
mahaifanta......nan dai yakwashe komai yafada mata
ayayin da taheer ke kwashewa a i pad dinshi shiko sadeeq
yama kasa wani kwakwaran motsi........
.
Bayan sun fitane tatashi tafada jikin abban ta .....kowa ya
tausaya mata domin hjya harda hawaye saida tayi amma
banda nafeesat da haushin samra takeji tunda taxo ....har
ALLAH yakara tayi mata axuciyar ta.....
.
Bayan sati 2 dafaruwan haka ne alkcn kowa yatafee taji
sauki sosai amma tana ta missin din fatee.....Alkcn ne ddy
yasamar mata mkrnta amma na kwana yayi haka ne domin
akwai wani aikin daxaa tura su na shekara 2 kuma baxaiso
yabar bby ahannun nafeesat ba domin yasan xata musguna
mata ne Haka dai yaje yayi mata registration dinta a
boardin skul....ho ho ho ranar da xai kaita tunda safe take
ta kuka.....haka yakaita mkrnta daxai tafee kuwa xuwa tayi
ta rungumeshi tana kuka shiko ranshi kamar sai fita kadan
ne yarage yayi kuka shima amma ya dake yanata bata hkri
tare da alkawarin xai dunga xuwa yana dubata kowani
ranar visitin......haka kuwa akayi duk ranar visitin sai yaxo
idan yatashi tafeeya kuwa sai tayi ta kuka shiko sai dai
yayita lallashi......cikin ikon ALLAH kuwa tagama first term
a ss1.....ranar da sukayi hutu kuwa driver ya turo yaxo
yadauketa don sati daya kenan da daurin auren shi da
nafeesat kenan har takai karanshi wajen alhji wai tunda
sukayi aure bai taba kula taba ....shine alhji yace a daren
yanaso yabata hakkinta dakuma karyakuma fita sai bayan
sati 2....shiyasa baije yadauko taba ya aika driver.....domin
fushi yakeyi tun ranar daya kusance ta yaga cewa bata xo
da budulcin ta ba ........amma yaukam sai murna yake don
bby xata dawo.....
.
Samra nadawowa tafita daga mota tana gudu tana abba
abba haba aishima da gudu yafito ai sai tarungumeshi
yadago da ita yace bby kin girma fa.....tace abba nihar
yanxun yarinya ce ahaka ne suka shiga cikin pallow tawuce
daki.......
.
BARA MULAKE MUGA MUMMYN SAMRA.........
Bayan sun gane cewa tana da ciki wato mutanen dasuka
dauketa suka soma bata kulawa ta mussamman ahaka dai
harta haifo yaranta twince duka maxa sukaci sunan arif da
afrab.......bayan haka ne suma mutanen dasuka tsinceta
suka samo mallami yamata rukiya suma aljanun daaka turo
mata suka fita.....amma tamanta duk abunda yafaru da ita
abaya....ahaka tacigaba daxama dasu hat ila ga yau kuma
tana samun kakkayar kulawa...... .

Read More »

NA MANTA KOMAI Part 2 & 3

NA MANTA KOMAI Part 2 & 3
.
Na H.m Jamo
.
GIDAN SU SUHAILA.
Aunty Rukayyah ce ta shigo d'akin ta na ta fad'a "Waike
Suhailah mi yake damunki ne? Ace tunda aka fara hidimar
aurenki ba ruwanki da komai, ba ruwanki da kowa! To
malama ba damu zakiyi fushiba da Dadyn ki za kiyi fushi,
shida kike ganin ya miki shishigi a rayuwa, ta qara so cikin
d'akin wai ma kina ina ne inata magana kinyi banza dani.?"
Turus tayi ganin ba Suhailah ba labarin ta, ta ja guntun
tsaki, ta lek'a bayi nan ma ba ta nan, "Ina yarinyar nan ta
shiga ne!?" Ta fito tsakar gida tana tambayar mutane ko
akwai wanda yaganta!? amma kowa yace rabonshi da ita
tun jiya, wasu kuma suce tun da asuba, nan da nan aka
bazama neman Amarya, amma bata ba labarin ta, aka kira
Dady akan ba Amarya fa kada a d'aura Aure, Dady yayi
murmushi, yace "Aure kam ba fashi sai an d'aura." Ahmad
ne yazo ya sami Dady, yace su kwantar da hankalin su
yasan gunda take, bayan d'aura Aure zaije ya d'auketa ya
wuce da ita, kawai a had'a mata kayan ta, sannan hankalin
danginta ya d'an kwanta, bayan d'aura Aure Ahmad yaje ya
d'auketa gunda tayi da Yusuf, tun lokacin da ta bude k'ofa
ta fara gudu ne ya kira Su ya sheda masu cewa ya ganta
kuma Suna tare lafiya lau. Sunji haushi, duk da cewa dama
ba wanda zai rakata Abujar amma sun so ko yar hud'uba ce
a mata harma yanda kan Suhaila yake rawa, amma hakan
bai samuba kuma ta kashe wayarta.. Bayan ya d'auketa sai
ya wucee da ita Abuja..
.
***********
Yana isa yayi parking din motar ya fito abinshi ya shige
gidan gonarshi. Amfi minti talatin da tsayawarshi, masu aiki
sun kwashe yan kayan Suhailah dake cikin motar, amma ita
Suhaila bata fitoba, a ranshi yace "wai yarinyar nan mi take
nufi ne??" ya koma wajen motar ya sa k'afa ya d'an shureta,
amma maimakon ta tashi sai ta qara juyawa tana
murmushi, ta cigaba da baccinta.
.
kilan Suhaila taci gaba da mafarkinta ne.... Tsaki yayi
aranshi yace "kyaji dashi yarinya kin riga kin zama matata"
komawar shi yayi cikin gida, yaje yayi wankanshi da ruwa
masu d'imi, yaji jikinsa yad'an warware da gajiyar tuk'i
yasamu guri ya kwanta sai bacci.!! Sai k'arfe biyu ya farka,
ya tashi ya lek'a d'akinta da ko ina amma bata ba labarin
ta, tsaki yaja wato har yanzu tana cikin motar kenan, ya
gane bata da niyar shigowa ciki, yaje gun motar ya kuwa
hangota tanata bacci abinta, bai ma tsaya bata lokacinshi
ba wajen tada ta, kawai d'auko ta yayi ya kaita d'akinta da
yasa aka gyara mata cikin d'akunan dake sama, ya ajiyeta,
a ranshi yace " Hmmm.!! mata akwai fi'ili ita kuma nata
borin kunyar haka take yinsa" .... Yayi d'an guntun tsaki
chikin ranshi ya kashe wutar d'akin ya wuce abinshi... Duk
da kasan cewar gurin gidan gona ne, gidan ya tsaru fiye da
tunaninku masu karatu, "ni kaina M. Jabo dana shiga gidan
saida naji kamar ace gidan J.S d'inane, habawa da zamu
soye a gurin ba kad'an ba dan zaiyi d'ad'in soyewa.."
Ahmad mutunne mai tsari, gaban shi da bayan shi, yadda
yake a tsare physically, haka duk wata harka tashi take a
tsare, haka mazauninshi abinshi gwanin burgewa...
.
YANDA ABIN YAKE AKAN YUSUF.
Bayan fitowar Yusuf daga wajen Suhaila, bai tsaya ko inaba
sai wajen Ahmad, ya gaya mashi duk yadda sukayi da ita,
abunda bai gaya mashiba kawai shine ya rungume ta, for
the first time (a karon farko)duk tsawon rayuwarsu, sanin
Ahmad ne da halinsa yasa ko giyar wake ya zuk'a bazai
furta ma Ahmad hakan ba.. Wannan sirrinshi ne har
kabarinshi sai ku masu karatu da ni Jabo yar gane-gane
dana gano... Ahmad yayi murmushi chikin ransa, yayi ma
Yusuf godiya ya dafa kafad'arshi ya wuce abinshi, aranshi
yake cewa "wannan yarinya daban mamaki take," ya karbi
makullen motar, amma bai tafiba a lokacin sai da aka
d'aura Aure akayi reception, mutane suka fara watsewa
Sannan ya kama hanya, Yusuf har ya fara jin Ahmad ya
bashi haushi a lokacin... Ya za'ayi ya ijiyeta awa sama da
biyu, bayan ya gaya mishi tana chan tana jira, tsaki yaja,
"duk nina janyo mata ai," duk da dai yasan bashida yadda
zayyi dashi tunda Kudin da Ahmad ya bashi duk rayuwarshi
ba wanda ya taba bashi su, duk akan ya kula mashi da duk
wani moves din Suhailah .....!!!
****************
Washe gari da Suhailah ta tashi daga bacci, ta tashi da
matsanancin ciwon kai, kuma duk inda ta juya jikinta ciwo
yake mata, tana Wash! Wash!! haka ta tashi dak'er ta
zauna, ta kalli nan ta kalli chan, bata gane ina take ba sam,
jeem tayi, ta dan girgiza kanta, amma bata gane komai ba,
ta ta shi ta rik'a tura k'ofofin da suke d'akin har ta gane
bandaki ta tura kai ciki, nanma kalle kalle ta rik'ayi sai kuma
ta tsaya kunne kunne, a ranta tanajin kamar akwai abinda
akeyi a gurinnan Amma bata gane ko miyeba, kuma tanajin
kamar akwai abinda ya dace tayi yanzunnan amma bata iya
tuna miye, lokacin taji cikin ta na k'ugi alamar yunwa takeji
kamar ta mutu, ta mik'e tsaye, ta nufi k'ofa kenan zata
bude idonta ya kai ga mirror d'in d'akin,duk abunnan sai
yanzu ta kula da fuskarta a mirror, ta kalli kanta sosai,nan
take gabanta ya fad'i tsoro ya kamata,ta tambayi kanta ta
madubi, ko Wacece wannan....." who are you..."abun
mamaki abun tsoro, ta kasa ba kanta amsa, ai kuwa sai ta
sa ihu, k'walla ne ke kwarara daga idanuwanta sabida
kukan da take baji ba gani......
.
Can cikin bacci Ahmad yaji ihunta, Ahmad da sauri ya fito
daga d'akinshi, a dai-dai lokacin da yayanshi Surayya da
Rukayyah suka fito daga nasu d'akin, suka iso inda yake
kowacce ta kama hannu d'aya Suna murje ido alamun
yanzu suka tashi daga bacci, had'e da murmushi a
fuskarsu, suna murnar ganin Dadyn su, dan jiya koda ya iso
sunyi bacci, suna isa dai-dai k'ofar d'akin Suhailah ta bud'e
k'ofar ta fito tana yan hawaye, daganinta duk a tsorace
take, yara kuwa da ganinta sai suka hau tsalle suna murna,
da sauri suka je suka rungume ta, suna "oyoyo Mumy!!!
oyoyo Mumy!!! " nan da nan Suhaila cikin dubara ta goge
k'wallan idonta.
.
Yaran sun bata sha'awa, ta d'anyi murmushi ta rungume su
itama, ita kam gaskiya tayi mata yawa, yanxu ita take da
way'annan yaran k'yawawa haka,..??? Rukayya ta juya
tace "Dady yaushe ka kawo mana Momy....??" yace "jiya
kuna bacci tazo..." Suhailah a aranta tace "Idan way'annan
y'ay'anane, kenan wannan shine mijinna...?" ta saki baki
tana kallon su ba tare da tasan takamaiman gaskiyar
abunda takeji ba, ta k'ara d'ago kai ta kalleshi aranta tace
"amma mijina fa ya had'u gaskiya, y'ay'anmu kuma masha
Allah, kamar y'ay'an larabawa" koda yake, itama Ba daga
bayaba wajen kyau... Yaran basu ko wanke baki ba suka ce
" Momy yunwa mukeji kuma Momy ke zaki bamu abinci,"
haka suka ja ta suna murna zuwa dinning table, da basu
kaita gurin ba, da batasan ko inane dinning table ba, kamin
su k'arasa Dady yace "kunyi brush kuwa??" Surayya tace "
no Dady, yanzu muka tashi," " maza ku wuce a muku
brush," "Dady mu Momy zata mana," suka fada suna kallon
Suhailah, sai ga wata mata ta fito, ta duk'a har k'asa ta
gaida Suhaila, ta amsa a sake, suka mak'ale ma Suhaila ala
dole ita zata musu, yace " kunsan dai ba zakuci abinci ba
sai kunyi brush" suka turo baki na shagwaba "Momy muje
ki rakamu" haka suka ja Suhaila tana kallo aka musu brush
sun k'i yarda a musu wanka, sannan suka fito, suna rik'e da
hannun ta, cike da nishadi.
.
Suka k'arasa ta bubbuda abincin, ta zuba musu dankali da
Egg tana basu Suna bata, itadai ci take amma bakinta wani
iri take jinsa tunda batayi brush ba, sukaci suka k'oshi
sannan sukace "Momy yau ke zaki mana wanka." haka
suka jata har bayin dakinsu, tace " kowa yayi wanka mu
gani kun iya wanka" ai kuwa suka fara wanka suna wasa da
ruwa, abin nema ya samu, saida suka gaji suka ce "mun
k'are suka fito, oya kowa ya shirya mu gani, suka shafa mai
kamar yanda sukaga nany dinsu tana musu, suka shirya
kansu tsaf cikin wando da riga mai kama da irin wanda ta
sanya, purple riga da black jeans. Momy kayan mu irin
d'aya da naki, Suhaila kam dadi take ta ji wai tanada 'ya'ya,
har biyu, yan mata dasu, aranta tace " kenan kullan haka
nake musu wanka na shiryasu? Gasu kyawawa dasu, tayi
murmushi, kyaufa yayi, har cikin zuciyarta takejin sonsu,
itakam har ta mance da ciwon da jikinta yake yi, duk da
yayi tsami sosai, kuma da d'an tabo a hannunta, ta kula
yaran akwai mai kula dasu, da kuma wata tsohuwa da ta
hango a gidan, amma batasan ko wacece wannan tsohuwar
ba. Rannar haka suka wuni tare da y'ay'anta, cike take da
nishadi, da ta d'auki Rukayya, sai Surayya ma tace sai ta
d'auketa, haka sukayi bacci a jikinta suna kallo a palo, ta
rasa gane komai itakam. Nanny dinsu tazo ta kwashe su ta
kai su d'akinsu, ta manta sam da ciwon da kanta da jikinta
keyi, sai da tayi shirin bacci sai tace bari tayi wanka itama,
ta shiga toilet itama tayi wanka, kamar yanda y'ay'an ta
sukayi, ta fito ta shafa mai, ta saka tufafi har a lokacin dai
ba ta jinta dai-dai ta kwanta ta fara tunanin wacece ita
haka!!!........
.
Ta kwanta sai juyi take, amma ba abinda yake zo mata, duk
tunanin duniya tayishi amma bata tuna komai akan kanta,
iyakanta abinda ya faru da ita yau take iya tunawa, yaranta
mijinta sai wankan da sukayi, juyi take tana baiwa
k'wak'walwarta wahala, Amma shiru, dagyar ta tuna wasu
abubuwan da tun tana shekara goma suka faru, daga nan
bata k'ara tuna komaiba. tashi tayi ta shiga dube- dube a
d'akin nata, ta bud'e wannan ta bud'e wan chan, anan taga
wasu littafai, ta dauko, abin mamaki sai taga tana iya
karanta wa, littafin da yafi jan hankalinta shine KULA DA
MIJINKI yanda ake kula da mijine, ta d'auko ta jujjuyashi
sai kawai ta koma bakin gado ta zauna, ta fara karantawa,
tanayi tana murmushi ita kad'ai, har saida ta karanceshi
tsab sannan ta koma ta kwanta... Bayan ta kwanta sai ta
fara tunanin ina mijinta? Tun ganin da tayi wa wai mijinta
da safe, bata sake ganinshiba, sai ta sauko k'asa, nan ta
zauna palo tana jiran isowarshi domin itafa kanta a d'aure
yake, gata matar aure harda miji uwa uba harda yaya biyu,
tirkashi!!!, dole tayi mashi tambayoyin da in ya bata amsa
zata iya gane ita wacece dan jinta takeyi kamar
TA MANTA KOMAI....
.
Tashin hankali baa sa maka rana,da alama dai Suhaila ta yi
loosing Memory d'inta ne a yanda na fahimta,... Can kuma
Ahmad, sai tunane-tunane yake shin abun nan, pritending
take kamar bata san komai ba, dan yasan kissar mata yawa
gareta, ko kuwa akwai wani abune?? Gani yake kamar ta
amincene ta zauna da shine a matsayin mijin nata, shine
take basarwa, to lallai yana ganin hakanne, ta amince ta
zauna dashine dinne, yayi dan murmushi wanda ya fito da
kyanshi a bayyane, kai mata akwai iyayi, kalli yanda ta
fuske kamar ba itaba a bayyane yace "Mata! Mata!! ya
kada kai ka barsu kawai....." Amincewa tayi dan ya zama
dole, domin kuwa bakin alk'alami ya riga ya bushe, an riga
an d'aura masu Aure shi da ita, kuma ba saki har abada,
Ahmad kenan da masu aikin gidansu suka saka masa suna
Alhaji Rabo..... Na zama mijin Suhaila kenan, yayi
murmushin da bai kai ciki ba, amma azuciyarshi har yanzu
inya tuna wasu abubuwa sai yaji wani baqain ciki da
zuciyarshi ke tafasa, kuma har yanzu ya kasa cire wannan
abu a zuciyar shi, wanda duk sadda ya tuno abin yake jin
zafi har yaji ya tsaneta, amma yayi ma mahaifinta
alk'awarin zai rik'eta amana a matsayin matarshi, amma ya
za'ayi yayi hakan,!? bai saniba har yanzu,!! Shiyasa lokuta
da yawa sai yaji Kamar yacema mahaifinta ya fasa
aurenta,amma kuma sai ya kasa....!!
*************
SHEKARA UKU DA SUKA WUCE
Shekara uku da ta suka wuce,... lokacin da mahaifan
Suhaila suka dawo daga umra, Ahmad tuni ya riga ya koma
k'asar Holland, basu sake haduwa da Ahmad ba, dan bai
sake zuwa Nigeria ba, sai lokacin da ya samu labarin
rasuwar yayan shi da matar yayan shi, sun kuma bar baby
dinsu Surayya Just 2month da haihuwa, yana nan gida
yazo ta'aziyyar yayan shi, sati daya aka yiwa Ahmad waya
aka gaya mashi ya dawo gida, domin matarshi na cikin
mawuyacin hali,rabon suyi sallama, yana isa akayi mata
C.S aka ciro babyn cikin ta, ita kuma ta rasu,ya sama Baby
dinsa Suna Rukayyah...sunanda matarshi takeso take kuma
k'auna kenan shi kuma ya saka mata Rukayyah..
********
Rasuwar yayanshi sunyi magana sosai da Alh Ibrahim
mahaifin Suhaila, inda ya gaya mashi abubuwan da yawa
da bai sani ba, wanda yake zaton shine yayan nashi ke
cewa zai gaya mashi, Amma kuma Allah ya masa cikawa,
asalin samun gonar da suke ciki yanzu kenan wadda da
tana hannun yayan nashi ne kamin ya rasu, duk makircin da
Alh ismail ke k'ullawa,wanda ya janyo accident d'in motar
yayan shi, ya yi sanadin rasuwar yayan nashi da matar
yayan shi, amma har yanzu dai ana kan bincike, dan a gano
gaskiyar abinda ya faru, wannan dalilin yasa Ahmad yasa
ya tattaro ya dawo gida don yaci gaba da harkar bussines
din mahaifinshi da yayan nashi.!! Ba'a dade ba, Alh Ibrahim
ya neme Ahmad da ya auri y'arshi y'ar autarshi Suhaila,
wacce duk cikin yaran shi yafi k'aunarta sabida tsananin
kama da takeyi da mahaifiyarsa. Ahmad kuwa ya kuma
amince da auren Suhaila amma ya amince ne bawai dan
yana sontaba hasalima ya tsaneta tun tana yarinya data
mishi wani abu, kawai dan ya lura Alh Ibrahim mahaifin
Suhaila mutun ne mai mutunci kuma shi kadai ya yadda
dashi a cikin abokan mahaifinsa, bayan an bashi Suhaila
akace kuma an bashi lokaci har sai ya shirya sannan ayi
auren, ************ A ranar a aka aje maganar auren sa da
Suhaila, Ahmad ya samu kanshi dayi ma duk mutanen dake
aiki a gidan su Suhaila, k'ananan ma'aikatan kampanin Alh
Ibrahim kyautar kud'i dubu goma goma, shi kanshi bai san
dalilin yin hakan ba, sai dai kawai ya tsinci kanshi cikin farin
ciki da annashuwa, dukda yasan bayason Suhaila, tun daga
ranar suka sa mashi suna Alhaji Rabo wanda kowa a gidan
da sunan yake kiransa Ita kuma marainiyar y'arshi da da
yar yayanshi, kakarshi da nanny dinsu ne suke kula dasu,
har suka dan girma, suka fara wayo kullun cewa suke
yaushe za'a kawo masu Momy d'insu, hakan yasa Ahmad
ya bijiro da xancen auren Suhaila, amma badan yana
sontaba, Su kuma yaran ganin Suhaila yasa suke tunanin
mamansu ce, ga kuma madam din TA MANTA KOMAI.
Sabida lokacin da zai tafi daurin auren haka yace masu
zaije ya kawo masu Momy dinsu....
**************
Cikin dare Suhaila ta farka cikin bacci amma ta kasa
motsi,gabanta ya fadi ita da ta kwanta a palo, miya kawota
daki, al'amarin ta fa sai d'ad'a jagule mata yake! "Waima
ina mijinta ne!?" Yayanta ne gabanta, Surayya ta rungumeta
a dama Rukayyah a hagu...tayi murmushi ta k'ara
rungumesu, babu shakka y'ay'anta na sonta, ashe suma
sun farka cikin darene suka dawo wajenta, gaskiyayarane
kyawawa babansu kyakykyawane, Itama ba daga baya ba,
ai kuwa dole su bada result mai kyau da haka bacci mai
d'ad'i ya k'ara kwashe ta.....
.
kira da Dady, itace yarinya ta hud'u kuma itace Auta, Dady
yana matuk'ar sonta ne sabida tsananin kama da sukeyi da
mahaifiyarsa. Asalinsu buzaye had'e da fulani, Alhaji
Ibrahim murzajjen d'an boko ne, irin masu tara suma dinnan
aka, yazo birni gun wani aiki na idanu, a k'auyen Tambuwal
cikin birnin Sokoto inda yaga gari ya masa sai ya dawo nan
da zama, anan k'auyen ya hadu da mahaifiyar su Suhaila,
har suka yi aure, ta haifa mishi yara hud'u mata biyu maza
biyu. Rukayyah itace babba, sai kuma Al- Ameen sai Suhaila
da Suhail wayanda su twins ne, sune k'anana. Harkar
gyaran ido ta karbeshi ba kadan ba, inda ya koma birnin
Sokoto da zama, anan ya had'u da Alhaji Isma'el, da kuma
Alhj Sulaiman sai aka koma kasuwanci. Alhaji Sulaiman
shine mahaifin Su Ahmad, yaransa biyar Mahmoud shine
babba, sai Zainab, sai kuma Ahmad da Fatima, sai autarsu
Khadija. Sun shaqu iya shak'uwa su ukunnan, tare suke duk
wata harka ta kasuwanci.
.
*********
Wata rana Ahmad ya dawo daga makaranta sai ya hango
kamar ana butsul-butsul a ruwa, har ya wuce sai kawai ya
dawo yana lek'awa sai yaga abin yayi yawa, koda ya matso
sai yaga mutum ne, baisan lokacin da ya fada cikiba ya
tsamota. Yarinya ce 'yar kimanin shekara 8, ya kwantar da
ita ya rik'a matsa mata cikinta a hankali tana fitar da
ruwanda tasha baki hanci, har ta fara tari, ta bude ido a
hankali, sai ta sake rufewa, Ahmad dai yaga abin ba nashi
bane sai ya d'auketa ya kaita gidansu, mamarshi na ganinta
ta fara salati, da yake ita tasan ta, "ina ka samo Suhaila ?? "
Yama Ammi bayani, " ai banga ta zama ba" ta dauko mayafi
ta yafa ta sungumi Suhailah sai gidan Alhaji Ibrahim ta
maida musu bayanin komai, Anata godiya, bayan kwana
biyu Suhaila ta ware waras, Mama ta kirata, "Ke wai garin
ya kika fad'a ruwa?" "Ba wannan ne ya turaniba!" Cikin
rashin fahimta Mama ta k'ara tambayarta, "wanene
wannan?" Suhaila kuwa ta tsaya kai da fata akan Ahmad ne
ya jefata ruwa, Mama cike da mamaki, take jimamin
lamarin, sai da Dady yazo ta mishi bayani abin da Suhailah
ta gaya mata, shikan bai yardaba sam, dan yasan halin
Ahmad tsab, dan haka bai d'auki maganar da mihimmanci
ba, mama ta yafa taje ta sami Hajiya Sa'adatu mahaifiyar
Ahmad ta bata labarin da Suhaila ta gaya mata, tace kawai
a jawa Ahmad kunne kada ya k'ara aikata irin haka, an
kuwa yi sa'a Ahmad yana gida, "kai Ahmady" na'am ya fito
d'akin su, cikin girmamawa ya gaida Mama, ta amsa a
sake, "dama Suhaila ce tace wai kai ka jefata ruwa ranar "
"waye Suhaila Ammi!?" Ya tambaya "yarinyar da ka kawo
shekaran jiya kace ta fad'a ruwa mana, har ka fito da ita"
shiru yayi chan kuma yace "akan me zan jefata ruwa
Ammi? Mi ta mini da zan jefata ruwa?" " mudai yanzu ba
wannan ne gaban mu ba, kawai ka fita harkar yarinyar nan
idan ba zaka taimaketa a matsayin k'anwarka ba, to kuwa
ka rabu da ita" Mama tace "kai tashi ka tafi abinka, kilama
shiririta ce irin ta Suhaila" cike da mamaki ya wuce d'akin
shi, lokacin Ahmad yanada shekara sha biyar, amma akwai
natsuwa gun shi, gashi komai nashi a tsare, iyayen sukaci
gaba da hirar su. Tun daga wannan rana Ahmad ya d'auki
tsanar duniya ya d'aurawa Suhaila, gashi ba wani saninta
yayiba dan ko ganinta yayi bazai ganeta ba, amma ko
sunan ta bayason ji wannan kenan....
.
***********
Da yake su uku suke kasuwancin su komai yana tafiya
yanda ya kamata duk da cewa Alhj Sulaiman shine
shugaba, dan kusan 50%(rabin dukiyar kaauwanci) dukiyar
shi ce, sauran rabin kuma na Alhaji Isma'el da Alhaji
Ibrahim ne. Alhaji Isma'el ya d'auki ki'yayyar duniya ya
d'aura musu ba tare da sun saniba, anan ne yayi nasarar
lik'awa Alhj Ibrahim satar kudin company kusan M.200,
kuma akayi bincike akaga kudin gurin Alhj Ibrahim, wanda
duk sharrin Alhj Isma'el ne, ba tare da wani dogon bincike
ba suka cireshi a shikinsu, suka dawo su biyu. Abin yama
Alhaji Ibrahim zafi ba kad'an ba, sharri harma na sata,
gashi da zuciya kamar me, bak'in cikin haka yasa yabar
Sokoto ya dawo Katsina da kasuwancin sa.
.
******************
BAYAN SHEKARA DAYA.
Alhaji Ibrahim yazo Sokoto ganin gida da iyalinsa anan ne
Suhaila ta sami accident ta fito daga gidan yayar ta
Rukayyah itada Suhail mota ta kad'e ta, shima Ahmad ya
fito gun wani cafe yaga mutane, yana zuwa yaga taro, ba
abinda akayi mata gata kwance, shida wani bawan Allah
suka samo taxi da police aka kaita asibiti, duk da ko lokacin
bai ganeta ba kuma bai kiyaye fuskar taba, wannan bawan
Allah ya gano iyayenta da taimakon suhail. Dady ya riga ya
koma Katsina, yace Rukayyah ta kula da ita dan ayyuka sun
masa yawa, an mata duk abinda ya dace.
.
Kullum Ahmad yana zuwa dubata, duk da baisan wacece
itaba, ranar ta tashi ta mik'e zaune yana zaune yana
karanta wasu takardu Anti Ruky na sak'a, dan mayyar sak'a
ce, tayita kallonsa, suna hada ido, sai ta masa murmushi,
tace " inasonka kaji " shima ya mata murmushi, yace " nima
inasonki" ta k'ara murmushi har haqoranta da take 6an6ara
suke bayyana "to zaka aureni idan na girma irin na Anti
Rukayyah da uncle?" Yace "Eh mana" yeeeee tace sannan
taci gaba, " to kaga Anti Rukayyah tana cema uncle Honey,
ni mi zaka cemini!?" "Aike kyakyawa ce so zan rik'a kiranki
da beautiful" ta zunburo baki "ni banason sunan, ko Dady
Some times (wani likaci yana cemin beauty, fadi wani mai
d'ad'i" ta ya mutsa fuska a yangace irin na yarinta, "kina
son Dear" a haf, ta d'auke kai gefe, tace "ai ko mama
tsohuwa dear take cema Dady" dariya yayi sosai har fararen
hak'oransa suka bayyana.....

Read More »

***** SAMRA 2 *****

***** SAMRA 2 *****
Samra dai tana tana jin musgunawa kala kala wurin umma
da umma taga dai baxata samu wani nasaraba kawai sai
takoma gun boka.....umma tace ma boka inaso yarinyan
nan tashiga duniya kamar uwarta kuma tamanta da
komai.....boka yace kande angama komai....kije gida
kihada ta damai mota ko direba ya kaita can nesa da gda ya
ajiyeta.....tace angama tadire mishi kudi tayi ficewar
ta.......bayan taxo gda ne taxo tasamu samra baiwar
ALLAH tayi tagumi allamu aljanu sun shigeta .....tayi
dariyan keta takira Aliyu direba tace xansa kakai samra can
nesa da gda ka jefar da ita ......kuma bana so kowa yaji
wannan mgnar inba haka ba inkasheka......Aliyu cike da
tsoro yace naji hjya......haka yadauki samra yasata amota
yakaita can nesa da gda sosai tausayin ta cike da xuciyar
shi ......ya juya xai tafee tace aliyu xaka tafee ne
kabarni....sbda hawayen daya cikarfin shi kasa cemata
komai yayi yaja motar yayi gaba........ Aliyu na tuki amma
tausayin samra yacika mishi xuciya kawai yaja motarshi
yaje gda yasamu ddy yadawo yanata tsoro kar ddy ya
tambayeshi samra .....
..
Amma shiko ddy tunda yadawo yamanta ma dawata
samra......itako umma har rawa tayi sbda murna tasan gida
yaxama nashi sai yanda tayi da gdan......bayan awa daya
da aliyu yadawo umma takara kiran shi akan kar taji
maganar abakin kowa inba haka ba sai ta kashe shi ne....
Bayan tafeeyar aliyu samra takife kai tana kuka naban
tasauyi .....koni danake zaune kusa da ita sai dana xubar
da hawayee......ahaka taxauna har dare yafara yi tarasa
yarda xatayi .....kawai tafara tafeeya can kuma tatuna babu
wanda tasani daxata je gdan shi......kawai saita dawo
takwanta agurin....wayyo samra...wuraren 9 nadare tana
kwance kawai taji an duketa tayi maza tatashi taga wani
haddadden mutum tsaye akan ta da kayan sojoji ......yana
kallon ta .....wato ABUBAKAR SADEEQ kenan.....bayan
yagama kallon tane yace mekikeyi anan tace wanine
yakawo ni ya ajiyeni anan....cann yagama tuna ninshi yace
taso muje kishiga mota muje .......kawai tafara kuka tana
roko shi da plx dont harm me am innocent......kawai y a
daka mata tsawa yace hu told am here 2 harm a smal girl
lyk u .....wil u stand up and get into d car.....haba ai dagudu
tayi cikin mota don tagama tsorata dashi.....
.
Tana shiga mota yaja motar xuwa gdan shi.....yana xuwa
yayi horn aka xo aka bude mishi....yaje yayi parkin sannan
yace sauka....tabude motar tasauka......yayi gaba tana
binshi a baya yashiga cikin gdan yakaita cikin wani daki
yace kiyi wanka inaxuwa tafada cikin bayi bayan yafita
daga dakin........tana shiga cikin bayin tayi wanka tafeeto
tana tsaye tana tunanin wana kaya xata saka.....kawai sai
gashi yashigo da kaya dakuma cream dasu kayan make
up......yace gashi inkin gama ina jiranki a pallow
........kawai yajuya yafeeta......yana feeta tasaka kayan
suka yi mata kyau taxubo gashinta har gadon bayan ta ta
fito.....
.
Yana ganinta tashigo pallow ya kalleta yace aransa kai
yarinyar nan kamar aljana take........taxo ta durkusa
agaban kafan shi.....yadago yakalleta yace mesunan ki
tace samra yace inane garinku tayi shuru yace mai yakawo
ki nan tayi shuru.......can dayaga batada niyyar mgna sai
yace xan saki amota gobe kikoma gda kinji koh ....tace toh
yace xauna akan kujera kici abinci......bayan sunci ne yace
jiki kwanta sai da safe......shiko saidaya gama dukka aduar
shi tukun ya kwanta.....da safe bayan ya tashi yace kije kiyi
wanka.......bayan tagama komai daxatayi ne .....yadauketa
xuwa tasha....yana ajeeyeta yabata kudin motar ta yace sai
wata rana....kawai yajuya yatafee..... Dayake kodaya kawo
ta tashan babu mutane dayawa acikin motar shiyasa
passenger suke xaune da tsaye a wajen motar.......itadai
tanata tunani inane ma hanyar gdan su .....can kuma
saitace toh ina kuma xani ma......shiko captain sadeeq
tunda yafara drivin nakomawa gda yake ganin kamar baiyi
adalci ba idan yabarta ta tafee kuma moreover shex til a
young girl haba ai tuni wani xuciyar tace kakoma kadauko
ta......nan da nan yajuya yaje yadauko ta wanda a daidao
lkcn ne suke shirin tashi......tana ganin shi tafara
kuka...shiko yana xuwa yajata xuwa mota kowa sai kallon
su suke sbda balain kama dasukayi da sadeeq......haka
yasata acikin mota yaja motar xuwa gda ita ko sai famar
rusa kuka takeyi.....yanaxuwa yayi horn akaxo aka bude
mishi yashiga cikin gate yaje ya ajiye motar sannan yace
budi kifita kije dakin ki...tana fita yaja motar sai wani super
market daya shiga yayi ta jeedo mata kaya both english nd
native wear ......haka ya juya kan motar sai gda..... Yana
isowa gda kai tsaye cikin dakinta ya shiga.....kawai yana
turo kofa ya ganta tana barci duk gashin ta ya rufe mata
fuska kuma ta takure kanta waje daya.....haba ai nan da
nan kawai ya gyara mata kwanciya....yaja mata kofa ya
fita....sai jajen 1 tatashi tafada bayi tayi wanka tayi alwala
don samra dukda kankantar shekarunta akwai tsabta uwa
uba kula da sallah......bayan ta idar ne tana xaune akan
darduma kawai sai ya bude kofa yashigo .....tayi maxa ta
durkusa a kasa tace sannu da xuwa ABBA sai yayi shuru
yana tunani wato har ya xama abbar ta lallai....can yace
kinyi wanka tace ehm yace wana kaya kika saka tace
nadaxun.....yace inaxuwa kawai sai gashi da cikin kaya
yace kixabi daya kisaka kisameni a pallow tace
toh......bayan yafita sai tayi maxa ta saka rigar tafeeta.......
Tana shiga pallow taxaune akasan kafan ta.....tace gani
abba.....samra tadago takalle shi yace ina mummyn ki da
daddyn ki...kuma inane gidan ku da garin ku .....ya gama
wannan tambayar taji kanta yafara mata ciwo.....can tayi
yunkurin xata bashi amsa amma ina kawai ganinta ne yayi
akasa ta fadi ta sume...dan danan hankalin shi yatashi yaje
yadauko ruwa swan mai sanyi daga fridge ya xuba mata
don danan tatashi.....tana xubar da kwalla...abun yabashi
mamaki amma sai yashareta bai kara ce mata komai
ba....Haka rayuwa takasance tsakanin sadeeq da samra
don babu wanda yasan xamanta agidan bbu wanda yasan
daxamanta a gdan .....ko iyayeshi da aboki shi wato
captain tahir wanda suke makota shima baisan da
xamanta....haka kuma idan har yatambayeta questions dan
gane da rayuwarta nada sai dai kawai kuganta
tasuma......haka dai ya hakra yabar ta badon ko sbda baya
sonji ba......amma yayi alkawari saiya taimaka mata...
.
WANENE ABUBAKAR SADEEQ
Sadeeq dai dane ga alhj bashir da hjy zainab.....shine da
na farko a family dinsu yanada kanni kuda 4 bayan shi
akwai muazzam,sadeeya,hafsat sai kuma autar su fateema
wato sa'ar samra kenan....amma tadan girmi samra da
shekara 2....suna zaune ne a garin kano...sadeeq dai yayi
primary,secondry nd tertiary instution dinshi a
abroad....bayan yadawo ne yace ma mahaifinshi cewa
yanaso yayi aikin sojoji..shine alhji ya tura shi military
skul...sadeeq dai yanada rike addini baya wasa da addinin
shi,yanada natsuwa,ga kyau,sai abu na karke miskili ne na
karke.....bakowa yake ganin dariyan shi ba saidai
mahaifanshi...ayanxun haka yana aiki ne a abja kuma yana
xaune ne agdan mahaifinshi dayake kaduna...dayake
mahaifin shi babbar mai kudi ne a garin kano...kuma
sunada son taimakon talakawa...sunada mutunci kuma
gdan su gdan mutumci ne.....KUNJI KADAN DAGA CIKIN
TARIHIN CAPTAIN SADEEQ KENAN.....
.
Haka dai suka ci gaba da rayuwa tsakanin sadeeq da
samra bawanda yasan da xamanta a gdan.....a lkcn wanu
shakuwa ne yashiga tsakanin sadeeq da samra yadauke ta
kamar his blood sister...itakuma tadaukeshi kamar abban
ta....amma duk da sonta dayake yi baya mata wasa inhar
tayi laifi....yanxun haka suna pallow yana kallon news da
misalin karfe 9pm ita kuma tana xaune akan cinyarshi tace
abba yace naam bby.....dama abba inaso ne kamar dani
skul ko kuma kasamomin lesson teacher.....yayi dariya ya
danyi kamo mata hanci ......yace acan gda wani klass kike
kawai gani yayi tasunkuyar da kai kawai sai ga hawaye nan
a fuskar ta yadagota yace com'on donr cry bby......suna
cikin haka ne suka ji sallamar captain tahir abokin abban ta
yace oya tashi kishiga ciki banason kowa yasan kina
nan.....haka tatashi tashi cikin daki .......sannan yayi ma
tahir iso zuwa cikin pallow.... ..

Read More »