Featured

Own A Blog Like This
For Questions, Inquiries, Click Here
Page | Group - Follow us - Call us - Hire Us - usamaumarusman1@gmail.com

Yanzu Yanzu: Allah yayi ma tsohon Sanata Kanti Bello rasuwa

Tsohon sanata daga jihar Katsina, Arewacin Najeriya, Kanti Bello, ya rasu.

Bello, wanda ya wakilci yankin Daura tsakanin shekarar 2003 da 2011, ya rasu ne a safiyar ranar Talata, 29 ga watan Agusta, 2017 a Abuja.

Tsohon shugaban rinjaye na majalisar dattawan ya rasu sakamakon wani rashi lafiya da ba’a tabbatar ba tukuna.

NAIJ.com ta samu labarin cewa Kabir Faskari, kanin tsohon mataimakin gwamnan jihar Katsina, Abdullahi Faskari, ne ya tabbatar da mutuwarsa a wata sanarwa.
“An umurci na sanar da kowa cewa munyi rashi na Sanata Kanti Bello a safiyar yau (Talata) a Abuja. Zaá sanar da yadda jana’iza zata kasance anjima.”

No comments

Post a Comment